Za a fara sakin gurɓataccen ruwa daga tashar nukiliya ta Fukushima

Asalin hoton, Reuters
Firaiministan Japan, Fumio Kishida, ya sanar da cewa daga ranar Alhamis za a fara sakin gurbataccen ruwa daga tashar makamashin nukiliya ta Fukushima.
Za a zubar da ruwan da ya kai yawan tan fiye da miliyan daya daga tashar zuwa tekun Pacific.
Wani da ke adawa da sakin ruwan ya bayyana cewa sakin ruwan bashi da wata matsala, amma ba su yi wani gwajin kimiyya a kan hakan ba.
Matakin sakin ruwan wanda hukumar da ke kula da makamashin nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shi a watan da ya wuce, ya fuskanci suka daga China da wasu 'yan Japan da Koriya ta Kudu.






