Wike ya yi barazanar rusa gidaje a ranarsa ta farko a ofis

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Kashi na 9 na ministocin da suka sha rantsuwa

    ...

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, ...

    Ministan wutar lantarki - Adebayo Adelabu

    Ministan harkokin tattalin arzikin teku - Adegboyega Oyetola

    Ministan kwadago da daukan aiki - Simon B. Lalong

    Ministan harkokin cikin gida - Bunmi Tunji-Ojo

    Ministan Babban Birnin Tarayya - Nyesom Wike

  2. An buƙaci gwamnatin Najeriya ta ayyana dokar ta-ɓaci kan maleriya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban kwamitin majalisar wakilai kan cutar HIV, tarin fuka, da zazzabin cizon sauro, Amobi Godwin Ogah, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kafa dokar ta-baci dangane da cutar zazzabin cizon sauro sakamakon mummunar illar da take yi wa ‘yan kasa.

    Ogah, mai wakiltar mazabar Isuikwuato/Umunneochi na jihar Abia, ya ce ya buƙaci hakan ne duba da irin barazanar da zazzabin cizon sauro ke yi wa al'umma, ya zama dole a mayar da hankali wajen kawar da sauro, wanda shi ne ya fi kashe mutane a duniya.

    Ya kara da cewa kwamitin majalisar na sane da kalubalen da ake fuskanta wajen yakar wadannan cututtuka kuma za su hada kai da masu ruwa da tsaki domin ganin an yi amfani da kudaden da aka ware yadda ya kamata.

    Ogah kuma ya bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su kara kaimi wajen kawar da sauro.

  3. Wasu ministocin da suka sha rantsarwa yanzu

    ...

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, ...

    Karamin Ministan Noma da Abinci - Aliyu Sabi Abdullahi

    Ministan yada labarai da wayar da kan jama'a - Muhammad Idris

    Ministan kula muhalli - Ishak Salako

    Ministan kudi da hadin kai na tattalin arziki - Wale Odun

    Ministan sadarwa da kirkire-kirkire da tattalin arzikin dijital - Bosun Tijani

  4. Wasu karin ministocin da aka rantsar

    ...

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, ...

    Ministar yawon bude ido - Lola Ade-John

    Ministan harkokin 'yan sanda - Imaan Sulaiman-Ibrahim

    Karamin ministan lafiya da walwalar jama'a - Tunji Alausa

    Ministan Karafa- Shuaibu A. Audu

    Karamin Ministan Ilimi - Yusuf T Sununu

  5. Karin ministocin da aka Rantsar

    ...

    Asalin hoton, Presidency

    Bayanan hoto, ...

    Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane - Abdullah T. Gwarzo

    Ministar fasaha da al'adu - Hannatu Musawa

    Ministan gidaje da raya birane - Ahmed M. Dangiwa

    Karamar Ministar Babban Birnin Tarayya - Mairiga Mahmud

    Ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki - Atiku Bagudu

  6. Yadda ake ci gaba da rantsar da ministoci

    ...
    Bayanan hoto, ...

    Wasu daga cikin ministocin da aka rantsar ya zuwa yanzu su ne:

    Ministan wasanni - John Eno.

    Ministan harkokin Neja-Delta, Abubakar Momoh.

    Ministan ayyuka - David umahi

    Ministan sufurin jiragen sama - Festus Keyamo

    Ministar bayar da agaji da kawar da talauci - Betta Edu

    Ministan ma'adanai, Dele Alake

    Ministan kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha - Uche Nnaji

    Ministan harkokin cikin gida - Sa’idu A. Alkali

    Ministan Masana'antu da ciniki da zuba jari - Doris Anite

    Ministan tsaro - Muhammed Badaru Abubakar

  7. An fara rantsar da sabbin ministoci

    ...

    Asalin hoton, VILLA

  8. Mun zaɓo ministoci ne bisa cancanta - Tinubu

  9. Sabbin ministoci sun fara isa wajen rantsarwa

    ...

    Asalin hoton, BOLA TINUBU?TWITTER

    Bayanan hoto, ...

    Ministocin da za a nada a Najeriya sun fara isa wurin da za a rantsar da su, yayin da suke shirin karbar mukamansu a hukumance da kuma fara ayyukansu.

    A cikin wannan wata ne Majalisar Dattijan Najeriya ta kammala amincewa da sunayen da Tinubu ya gabatar mata domin tantancewa a matsayin ministoci.

  10. Luisa Gonzalez ta samu nasara a zagayen farko a zaben shugaban kasar Ecuador

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, ...

    Yayin da aka kirga fiye da rabin kuri’un da aka kada a zaben shugaban kasar Ecuador, ‚yar takarar shugaban kasar Luisa Gonzalez ce ta samu nasara a zagayen farko da kuri’u fiye da kashi 33 cikin 100.

    Mai biye mata, shi ne dan kasuwar nan Daniel Noboa Azin da ya samu kashi 24 cikin 100 na kuri’un.

    A yanzu za a yi zagaye na biyu na zaben ne a watan Oktoba mai zuwa.

    Zabukan sun taso ne bayan shugaban kasar na yanzu Guillermo Lasso ya rushe majalisar dokokin kasar domin gudun kada a tsige shi.

    An yi yakin neman zaben kasar ne a cikin yanayi na tashe tahsen hankula da kuma rikicin ‘yan daba.

    Yawancin 'yan takara a zaben sun sanya rigar kariya daga harsashi da kuma hular kwano a lokacin da suka je kada kuri'unsu.

  11. An zargi Saudiyya da kashe 'yan ci rani

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, ...

    Kungiyar kare hakkin dan adam ta Human Rights Watch, ta zargi masu tsaron iyakar Saudiyya da kashe daruruwan 'yan ci ranin Habasha da suka yi kokarin tsallakawa don gujewa wuraren da ake yaki a Yemen cikin dabara.

    Ta ce masu tsaron iyakar sun kashe akalla mutane 650 tun daga farkon shekarar data wuce.

    Wata jami'a a kungiyar Nadia Hardman ta bayyana cewa masu tsaron iyakar Saudiyya sun harba abubuwan fashewa tare da harbin 'yanci rani da ma masu neman mafaka a kusa da iyakar kasarsu da Yemen.

    Kungiyar ta shafe watanni tana tattara shaida, bayan Majalisar Dinkin Duniya ta yi irin wannan zargi a bara.

    A watan Maris, gwamnatin Saudiyya ta yi watsi da duk wasu zarge zargen cewa dakarunta na da hannu a kisan da ake yi a iyakarta.

  12. Barkan mu da warhaka

    Masu bin mu a wannan shafi na kai tsaye, barkan mu da warhaka.

    Aisha Babangida ke fatan kuna lafiya a wannan safiya ta Litinin, inda za mu kawo muku labaran da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya bin shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke kawo muku.