'Jirgin yaƙi ya hallaka 'yan fashin dajin da suka kai hari Birnin Gwari'

Wannan shafi ne da zai rinƙa kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza, Nabeela Mukhtar Uba and Mukhtar Adamu Bawa

  1. Masu iƙirarin Jihadi a Mali sun ƙwace ɗaukacin Lardin Menaka

    Mali

    Asalin hoton, Reuters

    Masu iƙirarin jihadi a arewacin Mali da ke da alaƙa da ƙungiyar IS sun ƙwace iko da wani ƙauye a Menaka - wani lardi wanda akasari yanzu yake ƙarƙashin gudanarwarsu.

    Tun a farkon shekarar da ta wuce ƙungiyar IS ta babban yankin Sahara ta ƙaddamar da wani gagarumin hari a yankin da kuma a cikin Gao - wani lardin da shi yake arewacin Mali.

    Tidermene, ba wani babban ƙauye ne - matsuguni ne ga 'yan dubban mutane.

    Sai dai a yanzu, ya faɗa hannun mayaƙa masu iƙirarin jihadin da ke da alaƙa da IS, gwamnatin tarayya a ƙasar ta rasa iko da kusan ɗaukacin lardin Ménaka.

    Babban birnin lardin ne kawai har yanzu ake samun dakarun Majalisar Ɗinkin Duniya da sojojin Mali da kuma sojojin haya daga Rasha.

    Wani jami'in ƙauyen da ya tsere daga can ya tabbatar da ƙwace matsugunnin har ma ya ce 'yan ta-da-ƙayar-baya suna yawo ko'ina da makamai.

  2. Yadda gini mai hawa bakwai ya rufta a Legas

    Gini

    Wani gini mai hawa bakwai da ake ginawa ya rufta a yankin Banana Island da ke Ikoyi a jihar Legas.

    Jaridar Punch ta ruwaito cewa ginin ya ruguje ne dazu da rana.

    A cewar kafar yaɗa labaran, ginin ya rufta a daidai lokacin da wasu daga cikin masu aikin ginin suka tashi.

    Sai dai akwai wasu da rahotanni suka ce sun jikkata sakamakon lamarin.

    Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Legas, Amodu Shakiri ya tabbatar da faruwar al'amarin.

    Ya ce "mun samu kiran gaggawa da kusan ƙarfe 3:58pm. Muna ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da cewa babu wani da ya maƙale a ɓuraguzon ginin."

  3. EFCC ta damƙe mutum 11 da ake zargi da damfara ta intanet

    E

    Asalin hoton, EFCC/Twitter

    Jami'an hukumar EFCC mai yaƙi da yi wa arzikin ƙasa ta'annati sun cafke mutum 11 masu zamba ta intanet a Jere da ke ƙaramar hukumar Maiduguri a jihar Borno.

    Mutanen da ake zargi sun haɗa da Olatunji Sherif da Bright Felix da Jude Linus Magaji da Jonah Jondi da Ojobaro Abdullahi da Jerry Zizighi da Micah Joseph da Mari Ayuba da Ibrahim Abdullahi da Adam Abiodun da kuma Victor Chinonso Okolieaboh.

    An damƙe su ne bayan samun sahihan bayanan sirri game da laifukan da ake zarginsu da aikatawa.

    An kuma gano motoci da wayoyin hannu da wasu kayayyakin a hannun mutanen.

    EFCC ta ce za a gurfanar da su gaban kotu da zarar an kammala bincike.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  4. Syria za ta sake buɗe ofishin jakadancinta a Tunisia

    Syria za ta buɗe ofishin jakadancinta da ke Tunisia bayan fiye da shekara goma da kasancewarsa a rufe.

    Matakin ya zo ne sakamakon wata sanarwa da Shugaban Tunisia Kais Saied ya yi cewa ƙasarsa za ta sake buɗe ofishin jakadancinta a Damascus.

    Alaƙar Syria da ƙasashen Larabawa a yanzu ta inganta. Shugaba Bashar al-Assad ya kai ziyara Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da Oman kuma ya tattauna da Saudiyya.

    Gaba a wannan makon ne kuma, ƙasashen Larabawa tara za su gana a Riyadh domin tattauna batun kawo ƙarshen wariyar da ake nuna wa Damascus tun soma yaƙin basasa a Syria.

  5. Bayanan kwarmato: Dakarun Ƙasashen Yamma suna taya Ukraine yaƙi a cikin ƙasar

  6. 'Jirgin yaƙi ya hallaka 'yan fashin dajin da suka kai hari Birnin Gwari'

    El Rufai

    Asalin hoton, NASIR EL-RUFAI/FACEBOOK

    Wasu hare-hare ta sama sun yi nasarar hallaka 'yan fashin daji da ke tserewa a Birnin Gwari.

    Wata sanarwa da ma'aikatar tsaro da harkokin cikin gida ta Kaduna ta fitar ta ce an kashe 'yan fashin ne lokacin da suke tserewa bayan sun kai hari ƙauyen Sabon Layi a yankin.

    Ma'aikatar ta tabbatar da cewa 'yan fashin sun yi harbe-harbe a lokacin da suka kai hari Sabon Layi, tare da kore shanu da sace kadarori da kuma tafka miyagun ayyuka.

    A cewarta, abin da ya faru ya sanya mazauna ƙauyen rige-rigen tserewa don tsira da rayukansu.

    Sanarwar ta ce jirgin ya riski 'yan fashin ne a wani wuri mai nisan kilomita huɗu arewa da ƙauyen Sabon Layi, kuma nan take ya far musu.

    Tun da farko, wani shaida ya faɗa wa BBC cewa harin 'yan fashin dajin ya yi sanadin kashe mutum tara a yankin.

    Ma'aikatar tsaron Kaduna ba ta ce ga adadin 'yan fashin da aka hallaka a yayin luguden wuta da jirgin sojojin saman Najeriya ya yi ba.

  7. Dalilan APC huɗu na neman kotu ta soke zaɓen Abba Gida-Gida

  8. An kwashe 'yan Najeriya 152 da suka maƙale a Libya

    Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar kula da 'yan ci-rani ta duniya (IOM) ta kwashe 'yan ƙasar 152 da suka maƙale a Libya.

    Ofishin jakandancin Najeriya da ke Libya ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya aike wa manema labarai ta hannun jami'in ofishin.

    Jami'in ofishin ya ce wannan shi ne karo na uku da gwamnatin Najeriyar da haɗin gwiwar kungiyar kula da 'yan ci-rani ta duniya suke shiryawa a shekarar 2023.

    Lamarin dai ya kai ga kwashe kusan 'yan ci-ranin Najeriya 500 da suka maƙale a Libya.

  9. Dokokin masarautun jihar Kano da aka yi wa gyara

    Ganduje

    Asalin hoton, Kano state Gov.

    Majalisar dokokin jihar Kano ta yi wa dokar majalisar masarautun jihar gyaran fuska.

    Hon. Kabiru Hassan Dashi dan majalisa mai wakiltar mazabar Kiru, kuma mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar ta Kano ya shaida wa BBC abinda sabbin dokokin suka ƙunsa.

    Dan majalisar ya ce dokokin guda biyu ne, ɗaya gyara aka yi mata, yayin da ɗayar kuma sabuwa ce.

    Ya ce dokar da aka yi wa gyaran ita ce dokar majalisar masarautun jihar, inda dokar ta tanadi rage adadin mambobin majalisar masarautar daga 30 zuwa 17.

    Sannan kuma ya ce daga cikin gyare-gyaren dokar, daga yanzu kwamishinan 'yan sandan jihar da shugaban hukumar DSS na jihar da shugaban hukumar tsaro ta Civil Defence, da kuma shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin jihar, duk suna cikin mambobin majalisar masarautun jihar.

    A gefe guda kuma Hon. Kabiru ya ce an samar da sabuwar doka kan masarautun Gaya da Ƙaraye da kuma Rano, inda a yanzu sabuwar dokar ta tanadi cewa dole sai 'yan asalin gidan masarautun ne kawai za su yi sarauta a masarautun.

    ''Kamar dai yadda yake a masarautun Kano da Bichi inda doka ta tanadi cewa dole sai 'yan gidan Dabo ne kawai za su yi mulki a masarautun'', in ji shi.

    Dan majalisar ya ce su ma masarautun Gaya da Ƙaraye da Gaya an zaƙulo wasu mutane waɗanda tun asali su ne suke mulki a masarautun.

    ''Yanzu misali kamar gidan sarki Gaya akwai gidan Abubakar Sayyadi, gidan sarautar Rano kuma akwai sarki Ila, gidan Karaye kuma akwai gidan sarki Alu'', in ji shi

    A cewarsa waɗannan su ne gidajen da dokar ta ce dole sai waɗanda suka fito daga tsatson gidajen ne kawai za su riƙe sarautar masautun.

  10. An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Ghana

    n

    Asalin hoton, others

    Hukumar ƙididdiga ta ƙasar Ghana ta ce an samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki zuwa kashi 45 cikin 100 a watan Maris, maimakon kashi 52 cikin 100 da yake a watan Fabrairu.

    Ana alaƙanta saukar farashin da raguwar farashin abinci da aka samu da kashi 8 a watan da ya gabata.

    Wannan shi ne wata na uku a jere da ake samun saukar farashin kayayyaki a ƙasar.

    Tattalin arzikin ƙasar Ghana ya fuskanci koma-baya , a yayin da gwamnatin ƙasar ke ƙoƙarin samun tallafin dala biliyan uku daga Asusun Bayar da Lamuni na Duniya IMF.

    An sanya sabbin haraje-haraje a matsayin harajin gama-gari domin taimakawa wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar.

    Mutane da dama na ganin ya kamata gwamnatin ƙasar ta fara aiwatar da wasu sauye-sauye ciki har da rage naɗe-naɗen muƙaman gwamnati domin rage kashe kuɗin gwamnati.

  11. Yadda ake koya wa ƴan zamani kaɗa gangar Yarbawa

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
  12. An kama 'yan ci-ranin Habasha a Tanzania bayan da motarsu ta yi hatsari

    'Yan sanda a Tanzaniya na tsare da 'yan ci-rani 63 bayan kama su a kudu maso yammacin yankin Njombe a kusa da kan iyakar ƙasar da Malawi.

    Sugaban 'yan sandan yankin Njombe Hamis Issah ya ce an kama 'yan ci-ranin ne bayan da babbar motar da suke ciki ta yi hatsari a ƙarshen makon da ya gabata.

    Mista Issah ya ce kusan 'yan ci-ranin Habasha 100 ne suka yi sa'ar shiga ƙasar ta kan iyakar ƙasashen Tanzaniya da Kenya.

    'Yan ci-ranin Habasha da ke neman ingantacciyar rayuwa a Afirka ta kudu kan bi ta ƙasashen Kenya da Tanzaniya da Mozambique domin isa inda suke nufata.

    Kafafen yaɗa labaran ƙasar sun ruwaito cewa fiye da 'yan ci-rani 4,000 ne ake tsare da su a Tanzaniya, kuma ƙasar a shirye take domin mayar da waɗanda ke da muradi ƙasashensu.

  13. Girke-girken Ramadan: Yadda ake dafa mandi rice

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyo
  14. An gurfanar da tsohuwa a kotu kan laifin fashi a banki

  15. Ecowas ta kira da a saki yaran da aka sace a Najeriya

    Kungiyar Haɓɓaka Tattalin Arzikin ƙasashen Afirka ta yamma (ECOWAS) ta yi Alla-wadai da garkuwa da yara 80 a arewacin Najeriya cikin makon da ya gabata.

    Mafi yawan waɗanda aka yi garkuwa da su a jihar zamfara da ke arewa maso yammcin ƙasar, mata ne da yara waɗanda suka je sharar gona da yin itace a daji.

    A wata sanarwa, ECOWAS ta yi kira da a saki yaran. Kawo yanzu dai babu wanda ya ɗauki alhakin sace yaran.

    Harin dai shi ne na baya-bayan nan a jihar , wadda ke fama da yawaitar hare-haren 'yan bindiga masu sace mutane domin neman kuɗin fansa.

    A makon da ya gabata ma fiye da mutum 70 aka kashe a wasu tagwayen hare-hare a jihar Benue da ke tsakiyar ƙasar.

    A ranar Juma'a kuma wasu 'yan bindigar suka kashe gwamman 'yan gudun hijira bayan da suka kai wa sansaninsu hari.

  16. Yadda jami'an tsaro suka tsare Peter Obi a London

  17. Sojojin Nijar sun kama 'yan fashi a yankin Arlit

    'Yan fashi

    Asalin hoton, Arlit Division

    Dakarun sojin Nijar sun kama wasu 'yan bindiga da ake suna yin fashi a yakin Arlit.

    Hakan na zuwa ne a daidai lokacin wasu mahara da ba a san ko su wane ne ba, suka kai wa ayarin motocin sojin da suke yi wa masu haƙar zinare a yankin na Arlit rakiya.

    Lamarin da ya yi sanadin rasuwar sojojin ƙasar biyar, wasu biyar din kuma suka jikkata.

    Jajircewar dakarun ƙasar wajen kare al’ummomin yankin da dukiyoyinsu, na daga cikin sabbin matakan tsaron da sabon babban hafsan sojin ƙasar da aka naɗa a ƙarshen mako ya yi alƙawarin ɗauka.

  18. Yadda za ku gane sabuwar gwamnatin da za ta yi muku aiki

    Bayan kammala zaɓukan Najeriya yanzu hankula sun koma kan rantsar da sabuwar gwamnati.

    Shin kun san ta yadda za ku gane ko sabuwar gwamnati za ta yi aiki?

    Murtala Muhammed Adoge jami'i ne na wata ƙungiya mai taimaka wa gwamnati da ƙungiyoyi wajen samar da shirye-shirye na ci gaban ƙasa, ya yi bayani kan alamun da za ku iya gani idan gwamnati za ta yi muku aiki.

    Bayanan bidiyo, Latsa lasifikar da ke sama domin kallon bidiyon
  19. Jamus ta kori jakadiyar Chadi a matsayin ramuwar-gayya

    Mahamat Idris Deby

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Mahamat Idris Deby

    Ƙasar Jamus ta kori jakadiyar Chadi a ƙasarta a wani mataki na ramuwar gayya bayan da a makon da ya gabata ƙasar Chadin ta kori jakadan Jamus ɗin a ƙasarta.

    Ma'aikatar harkokin wajen Jamus ta bayyana a ranar Talata cewa dole Mariam Ali Moussa ta bar ƙasar cikin sa'o'i 48.

    A ranar Asabar ne jakadan Jamus a ƙasar Chadi Jan-Christian Gordon Kricher ya fice da ƙasar sakamakon korarsa da gwamnatin mulkin sojin ƙasar ta yi.

    Ƙasar Chadin ta zargi jakadan na Jamus, Jan Christian Gordon Kricher, da saɓa dokokin diflomasiyya da kuma rashin martaba hukumomin Chadi

    Mista Kricher ya kasance mai sukar lamirin gwamnatin mulkin sojin ƙasar wadda ke iko da ƙasar tun watan Afrilun 2021.

    Hukumomin Jamus sun ce Chadin ba ta bayar da takamammiyar hujjar korar jakandan nata daga ƙasar ba.

    Janar Mahamat Idriss Déby Itno - wanda ya ƙwace mulki bayan mutuwar mahaifinsa, Idriss Déby Itno a shekarar 2021 - shi ke jagorantar ƙasar a halin yanzu.

    A jawabinsa na farko da ya gabatar bayan hawansa karagar mulki, ya ce zai shirya zaɓe cikin wata 18 domin miƙa mulkin ƙasar ga farar hula.

    A yanzu gwamnatin ƙasar na shirin gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a shekara mai zuwa

  20. Ƴan wasa 32 na wata ƙungiyar ƙwallon ƙafa a Tunisia sun yi ƙaura zuwa Turai

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata ƙungiyar ƙwallon ƙafa a Tunisiya ta dakatar da ayyukanta bayan da duka 'yan wasan ƙungiyar 32 suka yi ƙaura zuwa Turai.

    Shugaban ƙungiyar Ghardimaou mai buga gasa ta huɗu Jamil Meftahi, ya yi zargin cewa 'yan wasan nasa sun bi ta teku ne da kuma ƙasar Sabiya kafin su tsallaka zuwa ƙasashen Turai.

    A baya dai 'yan Tunisiya ba sa buƙatar takardar izini kafin su shiga ƙasar Sabiya, har sai a watan Nuwamban da ya gabata.

    Shugaban ƙungiyar ya ce ba zai iya biyan 'yan wasan albashi ba, sakamakon matsin tattalin arziki da ƙasar ke fuskanta.

    Ƙasar Tunisiya ta kasance wata matattara ko tashar jiragen ruwan da ke dakon 'yan ci-rani zuwa Turai.

    Shugaban ƙasar Kais Saied ya yi watsi da tayin dala biliyan 1.9 na tallafi da Asusun Bayar da Lamuni na Duniya IMF ya yi masa, sakamakon ƙa'idojin tsuke bakin aljihu da tallafin ke ƙunshe da shi.