Tinubu ya tafi hutu zai kuma wuce Saudiyya Umrah - Kakakinsa

Wannnan shafi ne dai kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza

  1. Girgizar ƙasa ta hallaka mutum 12 a Pakistan da Afghanistan

    www

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla mutum 12 ne suka mutu fiye da 200 suka jikkata bayan da wata girgizar ƙasa mai ƙarfi ta afka wa wasu yankunan ƙasashen Pakistan da Afghanistan.

    Girgizar ƙasar mai ƙarfin maki 6.5 ta lalata gine-gine da nutsewar gidaje, tare da tilasta wa mutane barin gidajensu.

    Lamarin ya faru ne ranar Talata da yamma a tsakiyar lardin Laghman da ke arewa maso gabashin Afghanistan kusa da kan iyakar Pakistan.

    An jiyo ƙarar girgizar daga garuruwa da dama a ƙasar.

    "Girgiza ce mai tayar da hankali. Ban taɓa jin ƙarar girgizar ƙasa, kamar wannan ba a rayuwata,'' kamar yadda wata mazauniyar birnin Kabul ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP, bayan ficewarta daga gidanta na bene mai hawa biyar.

    An tabbatar da mutuwar mutum tara a yankin Khyber Pakhtunkhwa da ke Pakistan Pakistan.

    Sauran mutum ukun ciki har da ƙaramin yaro sun mutu ne a Afghanistan, kamar yadda mai magana da yawun ma'aikatar lafiyar ƙasar ya bayyana.

    Mutane da dama ne ke kan titunan biranen ƙasar domin murnar bikin sabuwar shekarar al'adar ƙasar a lokacin da girgizar ƙasar ta auku.

    Ma'aikatan agaji a lardin Khyber Pakhtunkhwa sun ce ɓarnar da girgizar ƙasar ta haifar ba ta kai yadda aka yi tsammani ba.

  2. Manyan jam'iyyun adawa sun shigar da ƙara don ƙalubalantar nasarar Tinubu

    Tinubu

    Asalin hoton, Google

    Jam'iyyun adawa hudu a Najeriya sun shigar da ƙara domin ƙalubalantar nasarar zaɓaɓɓen shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar 25 ga watan Fabrairun da ya gabata.

    Dan Takarar jam'iyyar PDP Atiku Abubkar da na LP Peter Obi da na AA Solomon Okangbuan da kuma na jam'iyyar APM Chichi Ojei duka sun shigar da ƙara gaban kotun ƙorafin zaɓe domin ƙalubalantar nasar Tinubu sa'o'i kafin cikar wa'adin da kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su dama na ƙalubalantar sakamakon zaɓen.

    Manyan 'yan takarar hamayyar biyu Atiku Abubakar da Peter Obi sun nemi kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen da ta ayyana cewa Tinubu bai ci zaɓen da aka gudanar ba.

    Peter Obi ya yi zargin cewa an yi aringizon ƙuri'u a jihohin Rivers da Legas da Taraba da Benue da Adamawa da Imo da Bauchi da Borno da Kaduna da kuma jihar Plateau.

    Obi na buƙatar kotun da ta ƙwace takardar shaidar cin zaɓe da hukumar INEC ta ba shi, tare da ba shi sabuwar takardar shaidar cin zaɓe.

    Ranar Talata da yamma ne Amurka ta fitar da wata sanarwa tana mai Allah wadai da ƙaruwar razanar da masu kaɗa ƙuri'a da sauran laifukan zaɓe da ta ce an aikata a lokacin zaɓen gwamnoni na ranar 18 ga watan Maris.

  3. Buhari ya ƙi sanya hannu kan dokar da ta bai wa majalisa damar gayyatar shugaban ƙasa

    r

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban majalisar dattawan Najeriya Sanata Ahmad Lawan, ya ce majalisar za ta sake nazarin sauran dokoki 19 da majalisar ta gyara wa fuska, waɗanda kuma shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya ƙi sanya wa hannu.

    Sanata Lawan ya bayyana haka a lokacin zaman majalisar na ranar Talata.

    A cikin watan Janairun da ya gabata ne majalisar ta aike wa shugaba Buhari wasu dokoki 35 da majalisar ta yi wa gyaran fuska, domin amincewa da su.

    To sai dai a makon da ya gabata shugaban ƙasar ya amince da dokoki 16 cikin 35 din da ta aike masa.

    Sanata Lawan ya ce ɗaya daga cikin sabbin dokokin da shugaban ƙasar ya sanya wa hannu ita ce dokar da ta tanadi samar da 'yancin gashin kai a ɓangaren kashe kuɗade ga majalisun dokokin jiha da ɓangaren shari'a.

    To sai dai ɗaya daga cikin dokoki dokoki 19 da shugaban ƙasar ya ƙi sanya hannu a kai har da dokar da ta bai wa majalisar dokoki ta ƙasa da majalisun dokokin jihohi damar gayyatar shugaban ƙasa ko gwamna, domin yin bayani kan wasu abubuwan da majalisar dokoki ta ƙasa ko majalisun dokokin jihohi ke da damar aiwatarwa.

    Da kuma dokar da aka yi wa gyaran fuska wadda ta tanadi tilasta wa shugaban ƙasa ko gwamna bin umarni ko yin biyayya ga gayyatar da majalisa ta yi masa.

  4. Assalamu alaikum

    Masu bin mu a wannan shafi barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba, Abdullahi Bello Diginza ne zai kasance tare da ku a wannan shafi na kai-tseye.

    Inda za mu ci gaba da kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.