INEC ta bayyana zaɓen gwamnan Adamawa a matsayin wanda bai kammalu ba

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa kan sakamakon zaɓen gwamnonin jihohin Najeriya

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza, Nabeela Mukhtar Uba and Buhari Muhammad Fagge

  1. An ci gaba da karɓar sakamakon zaɓen gwamnan jihar Rivers

    zabe

    Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ci gaba da karɓar sakamakon zaɓen gwamna a jihar Rivers da ke kudu maso kudancin Najeriya.

    A jiya an karɓi sakamakon zaɓen daga ƙanana hukumomin jihar 17

    A yanzu kuma da safiyar nan an ci gaba da ƙarbar sakamakon inda aka karɓi kananan hukumomi duɗu.

    Ga kuma yadda sakamakon nasu ya kasance:

    Karamar hukumar Obio Akpor

    A - 674

    APC - 7361

    LP - 8262

    PDP - 45065

    SDP - 3056

    Karamar hukumar Port Harcourt

    A - 981

    APC - 8954

    LP - 4660

    PDP - 26892

    SDP - 3974

    Karamar hukumar Degema

    A - 261

    APC - 3107

    LP - 102

    PDP - 4437

    SDP - 579

    Karamar hukumar Akuku Toru

    A - 698

    APC -3724

    LP - 61

    PDP - 6273

    SDP - 222

  2. Yadda magoya bayan NNPP suka riƙa murnar cin zaɓen gwamna a Kano

    vbv

    Daruruwan magoya bayan jam'iyyar NNPP ne suka fantsama kan titunan birnin Kano bayan da hukumar zaɓen ƙasar ta ayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar.

    bgn

    Abba Kabir Yusuf ya samu nasara ne da ƙuri'a 1,019,602.

    nj

    Abba Kabir Yusuf da ake yi wa laƙabi da Abba Gida-gida ya doke babban abokin hamayyarsa Nasiru Yusuf Gawuna na jam'iyyar APC mai mulkin jihar, wanda ya samu ƙuri'u 890,705.

    bb
  3. 'Yan sanda na murƙushe masu zanga-zanga a Kenya

    Kenya

    'Yan sanda a Kenya suna amfani da ruwan zafi da kuma barkonon-tsohuwa domin tarwatsa masu zanag-zanga a Nairobi babban birnin kasar.

    Babban ɗan adawan ƙasar, Raila Odinga ne ya yi kira a gudanar da zanga-zanga saboda zargi marar hujja kan cewa an ƙwace masa zaɓen da ya lashe.

    Sannan ya zargi gwamnati da kasa yin kataɓus wajen magance matsalar hauhawar farashin kayayyaki.

    A unguwar Kibera mai dimbin magoya bayan Mr Odinga, 'yan sanda sun yi arangama da masu zanga-zanga.

    Kenya
    Kenya
  4. Sha'aban Sharada ya taya Abba gida-gida murnar lashe zaɓe

    d

    Dan takarar gwamnan jihar Kano ƙarƙashin jam'iyyar ADP Sha'aban Ibrahim Sharada ya taya zaɓaɓɓen gwamna jihar Abba Kabir Yusuf murnar lashe zaɓe.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa Facebook, Sha'aba Sharaɗa ya yaba wa hukumar INEC da cewa ta yi abinda ya kamata.

    Da safiyar ranar Litinin ne hukumar zaɓen jihar ta ayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaɓen bayan samun ƙuri'u mafi rinjaye.

    Sha'aban Ibrahim Sharada na jam'iyyar ADP ya samu ƙuri'a 9,402 a zaɓen da aka gudanar.

  5. Bala Kaura ya sake lashe zaɓen gwamnan jihar Bauchi

    dsd

    Gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulƙadir Kauran Bauchi na jam’iyyar PDP ya sake lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar.

    Jami’in tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar, Farfesa Abdulkarim Sabo Mohammed ya ce Bala Ƙaura ya samu nasara ne da ƙuri’u 525,280.

    Ya doke babban abokin hamayyarsa Air Marshal Abubakar Sadique Baba na jam’iyyar APC wanda ya samu ƙuri’u 432,272.

    Jihar Bauchi dai na ɗaya daga cikin jihohin da fafatawa ta yi zafi a zaɓen gwamnonin a Najeriya.

  6. Abu takwas game da Abba Kabir Yusuf zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano

  7. An sanar da sakamakon zaɓen gwamna a ƙananan hukumomi biyar na Zamfara

    Zamfara

    Asalin hoton, others

    Hukumar zaɓe a jihar zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya ta karɓi sakamakon zaɓen gwamna daga ƙananan hukumomi biyar daga cikin ƙananan hukumomi 14 na jihar.

    Kuma sakamakon zaɓen da INEC ɗin ta karɓa a cibiyar tattara sakamakon zaben da ke birnin Gusau ya nuna cewa Dauda Lawal Dare na PDP ne ke gan gaba a yawan ƙuri'u.

    Takarar dai ta fi zafi ne tsakaninsa gwamnan jihar mai ci Muhammad Bello Matawalle na jam'iyyar APC, da Dauda Lawan Dare na PDP.

    Ga sakamakon ƙananna hukumomi biyar da aka klarɓi sakamakonsu a cibiyar tattara sakamakon da ke birnin Gusau:

    Ƙaramar hukumar Anka

    APC - 10,156

    PDP - 17,116

    Ƙaramar hukumar Bukkuyum

    APC - 10321

    PDP - 24,341

    Ƙaramar hukumar Zurmi

    APC - 21,027

    PDP - 24,328

    Ƙaramar hukumar Bungudu

    APC - 24,865

    PDP- 47,464

    Ƙaramar hukumar Gummi

    APC - 20,263

    PDP - 27,929

  8. A A Sule ya sake lashe zaɓen jihar Nasarawa

    AA Sule

    Hukumar zaɓen Najeriya ta ayyana gwaman jihar Nasarawa da ke tsakiyar Najeriya Abdullahi Sule na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar.

    Jami'in tattara sakamakon zaɓen gwamnan jihar Farfesa Tanko Ishaya ne ya bayyana haka, inda ya ce Abdullahi sule na APC ya lashe zaɓen bayan da ya samu yawaun ƙuri'u 347,209.

    Abdullahi Sule ya doke babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP David Ombugadu wanda ya samu ƙuri'a 283,016.

  9. Ana dakon sakamakon zaɓen gwamna a jihohin Adamawa da Bauchi da Kaduna

    zabe

    Har yanzu ana ci gaba da dakon sakamakon zaɓen gwamna a jihohin Kaduna da Adamawa da Bauchi.

    Tun a ranar Lahadi ne dai aka fara karɓar sakamakon zaɓen a faɗin jihohin Najeriya da aka gudanar da zaɓen gwamna.

    A jihar Adamawa 'yan hatsaniya ce ta kaure tsakanin wakilan jam'iyyu a zauren tattara sakamakon zaɓen, lamarain da ta sa jami'in tattara sakamakon zaɓen ya ɗage aikin karɓar sakamakon zaɓen zuwa yau da safe domin ci gaba da karɓar sakamakon.

    Jihar Adamawa na ɗaya daga cikin jihohin da fafata ta yi zafi tsakanin gwamnan jihar mai ci Ahmadu Umaru Fintiri na jam'iyyar PDP, da kuma Sanata Aishatu Dahiru Ahmed Binani ta jam'iyyar APC.

    Haka ma a jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin ƙasar ana ci gaba da dakon sakamakon ƙananan hukumomin da suka rage.

    Can ma a jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin ƙasar nan gaba kaɗan ne ke sa ran hukumar zaɓen za ta ci gaba da karba tare da bayyana sakamakon zaɓen jihar.

    Tuni dai hukumar zaɓe a wasu jihohin ƙasar ta bayyana sakamakon zaɓen na gwamna a jihohin Kano da Gombe da Katsina da Sokoto da Yobe da Jigawa da sauransu

  10. Assamalu alaikum

    Masu bin mu a wannan shafi barkan mu da sifiyar wannan rana ta Litinin, inda za mu ci gaba da kaso muku labaran sakamakon zaɓen sauran jihohin Najeriya.

    Abdullahi Bello Diginza ne zai kasance tare da ku a daidai wannan lokaci

    Kuna iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa