'Dole Taliban ta mutunta fararen hula'
A tattaunawar da suka yi tsakaninsu, shugaba Joe Biden da Firai ministan Birtaniya Boris Johnson sun tattauna kan muhimmancin amfani da matakin diflomasiyya da agaji domin kaucewa sake dagula lamura a Afghanistan.
Mai magana da yawun Mr Johnson ya ce shugabannin biyu sun amince duk wani mataki da kasashen duniya za su dauka, dole Taliban ta mutunta hakkokin farar hula.
Sun kuma tabo batun kasuwanci maras shinge a tsakanin kasashen biyu, a tattaunawar ta tsahon minti 90
Yace za mu tattauna kan batun kasuwanci a ranar Alhamis, batu ne mai muhimmanci. za a cimma matsaya kan wannan batu nan ba da jimawa ba.