Duk da bayanan da sojin kasar da jam'iyyar ZANU PF mai mulki ta yi, wakiliyar BBC Shingai Nyoka ta ce yanayin na da "dukkan alamun juyin mulki."
"Akwai bude wuta da kuma tashin abubuwa masu fashewa a unguwanni da dama cikin dare, ciki har da wuraren da manyan jami'an gwamnati suke zaune da kuma inda gidan Shugaba Mugabe da kansa yake.
"Sojin dai ta ce yana cikin halin lafiya kuma sun tabbatar da cewa zai kasance cikin tsaro.
"Sun ki yarda cewa juyin mulki ne domin ba su karbi iko ba. Sun ce sun yi hakon mutane da ke kewaye da shi ne kuma za su mayar da shi shugabancin kasar da zarar sun kammala aikinsu."