Hajj 2021: Hotunan yadda aka gudanar da tsayuwar Arafa a Muna

An wallafa

A ranar Litinin 19 ga watan Yulin 2021 wanda ya yi daidai da 9 ga Zul Hijja ne aka yi tsayuwar Arafa ta bana.

Dubban Musulmai ne suka yi hawan Arfan a Mina, kusa da birnin Makkah na Saudiyya, a matsayin ɗaya daga cikin muhimman ibadu na aikin Hajji.

Mahajjatan sun shafe sa'o'i da dama a filin na Arfa kuma a filin na Arfa ne Manzon Allah (SWT) ya yi huɗubarsa ta ƙarshe.

Kamar bara, a bana ma kasar Saudiyya ta taƙaita yawan Musulman da za su yi aikin hajjin zuwa mutum 60,000 kuma wadanda dama mazauna kasar ne kawai, a maimakon mutum kusanm muliyan uku da kan yi a duk shekara.

Manufar ita ce takaita yaduwar cutar korona.

Ga wasu zaɓabbun hotuna na yadda tsayuwar Arafan ta kasance.

Dukkan hotunan haƙƙin mallakar Getty IImages da Haramain Sharifain ne.