Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Zaben Amurka: Ƴan asalin Najeriya da suka lashe kujerun majalisa a Amurka
Hukumar da ke kula da ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje ta taya wasu ƴan asalin ƙasar da suka yi nasarar lashe kujerun majalisa a zaɓen Amurka.
Oye Owolewa ya kasance ɗan asalin Najeriya na farko da aka zaɓa a majalisar Amurka domin wakilar Washington.
Mista Owolewa ya lashe kujerar majalisar wakilai ƙarkashin jam'iyyar Democrats.
Haka ma Esther Agbaje ƴar Democrats ta samu kujerar majalisa a jihar Minnesota.
Shugaban hukumar kula da ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje Abike Dabiri-Erewa, ta wallafa sakon taya murna ga ƴan asalin Najeriyar kan nasarar da suka samu a zaɓen na Amurka.
Ta kuma ce sun kasance wakilai na ƙwarai abin koyi ga matasan Najeriya.
Abubuwa huɗu game da Esther Agbaje
- An haifi Esther Agbaje a Minnesota.
- Iyayenta, John da Bunmi ƴan asalin Najeriya ne da suka haɗu a Amurka a makaranta.
- Ta yi karatun shari'a a makaranta sharia ta Harvard Law school kuma ta ƙware ne a ɓangaren da ya shafi gidaje.
- Ta yi aiki a gwamnati a ma'aikatar harakokin wajen Amurka.
Abu huɗu game da Oye Owolewa
- Oye Owolewa ɗan asalin jihar Kwara ne a Najeriya.
- Ya yi digirinsa na uku a jami'an Northeastern Boston
- Ba wannan ne karon farko ba da ya shiga siyasa, ya taba zama kwamishina a kudu maso gabashin Washington a 2018.
- Burinsa a matsayin ɗan majalisa shi ne kawo sauyi a jiharsa.
- Yana son kawo ƙarshen haramta wa baƙi shiga ƙasar.