Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Coronavirus ta harbi mutum 5,959 a Najeriya, 1,594 sun warke
Sabbin alkaluma da hukumar dakile cutuka masu yaduwa a Najeriya ta fitar a daren Lahadi sun nuna cewa masu dauke da korona yanzu haka a kasar sun kai 5,959.
Wannan ya biyo bayan samun karin mutum 338 da suka sake kamuwa da cutar a cikin sa'o'i 24 da suka gabata.
Yanzu dai adadin mutane da cutar ta hallaka a fadin kasar ya kai 182, yayinda mutum 1,594 suka warke.
A Legas, jihar da ta fi yawan masu fama da korona, sabbin alkaluma sun nuna an sake samun mutum 177 da suka kamu.
Jihar Kano ita ce ta biyo a jadawalin daren Lahadi da mutum 64 sabbin kamu.
Birnin Tarayyar Abuja ke mataki na Uku da mutum 21, a jihar Oyo an samu mutum 11.
Jihar Katsina na da mutum 9, Jigawa na da mutum 4, haka ma Kaduna an samu mutum 4.
Haka kuma, mutum 3 sun sake kamuwa da cutar a Abia, Bauchi da Borno ma kowanne na da mutum uku-uku.
Akwai jihohin Gombe da Akwai Ibom da Delta kowane na da biyu-biyu.
Sai kuma Ondo da Kebbi da Sokoto da ke da mutum guda kowanne.
Muhimman bayanai kan annobar korona
An fara gano cutar korona a Najeriya ne a jikin wani baturen kasar Italiya ranar 27 ga watan Fabrairu bayan ya shiga kasar ta filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Legas.
Shi da mutum na farko da ya kamu da cutar ranar 20 ga watan Maris a arewacin Najeriya, Mohammed Atiku duk sun warke kuma an sallame su daga asibiti.
A ranar Juma'a 17 ga watan Afrilu ne cutar korona ta yi sanadin mutuwar Malam Abba Kyari, shugaban ma'aikatan fadar shugaban Najeriya. Shi ne mutum mafi girman mukami da ya mutu dalilin korona a kasar.
Gwamnoni irinsu Bala Mohammed da Nasir El-rufa'i da kuma Seyi Makinde na jihar Oyo duk sun kamu da annobar kafin su warke daga bisani.
Har yanzu a hukumance ba a samu bullar cutar a jihohin Kogi da Cross river ba, amma wasu na da ra'ayin cewa hakan ta faru ne saboda ba a gwajin cutar a cikin johohin biyu.
Hukumomin Najeriya dai sun ce sun rubanya adadin gwaje-gwajen da suke yi a kasar, inda a yanzu suka ce akan yi gwaji kimanin dubu guda cikin sa'a 24.
Ga jerin bayanan jihohin da korona ta bulla cikinsu ya zuwa daren Asabar 15 ga watan Mayu.