Ƙayatattun hotunan Afirka daga 8 zuwa 14 ga watan Mayun 2020

An wallafa

Zaɓaɓɓu kuma ƙayatattun hotuna daga NahiyarAfirka na wannan makon da kuma wasu sassa:

Wani dan ciranin kasar waje sanye da hankici ruwan dorawa, yana zaune ne a wani gini a yankin Kwa Mai Mai da ke Juhannesberg, ranar 10 ga watan Mayu 2020.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A ranar Lahadi a birnin Johannesburg na Afrika ta Kudu, wani mutum sanye da hankici ruwan dorawa a wani lungu a tsaye.
Wani mutum a wani kanti da akai wa feshin magani a Dakar a ranar 11 ga watan Mayu 2020. yayin da aka ba da umarnin rufe shaguna na wasu ranaku domin yi musu feshin dakile yaduwar cutar korona.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A ranar Litinin an share wani babban kantin zamani a Dakar babban birnin Senegal, yayin da aka ba da umarnin a rufe duka shaguna na wasu ranaku a wanke su sosai.
Wani mutum sanye da kayan kariya na leken waje ta cikin jirgin China da ya kai tawagar kwararrun kiwon lafiya daga China, da zasu tai maka musu wajen yaki da cutar Covid-19, an kawo kayan ma'aikatan lafiya filin jirgin sama na Robert Mugabe da ke Harare ranar 11 ga watan Mayu 2020.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A dai wannan rana kwararru a fannin kiwon lafiya suka isa Zimbabwe don taimaka wa kan yaki da cutar korona.
Ma'aikaciyar jinya ta sa kai, Anita Thumbi daga hagu wacce aka zaɓa a matsayin mamba a majalisar dokoki a lardin gwamnatin Nairobi, tana kula da wata mara lafiya don nuna wa mutane yadda ake kare kai daga kamuwa da cutar korona a wata cibiyar lafiya da ke Waithaka, a ranar 12 ga watan Mayu 2020, a yayin bikin ranar ma'aikatar jinya ta duniya.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A rana ta gaba a Kenya, 'yar siyasa Anita Thumbi na aikin jinya na sa kai tana kula da wata mara lafiya da ke fama da cutar korona.
Musulmai a masallaci sun kama wajen yin sallah tare da bin dokar ba da tazara tsakani bayan sake bude ,masallatai a karon farko cikin wata biyu a ranar 12 ga watan Mayu 2020. - Wannan na zuwa ne bayan shugaban kasar Senegal, Macky Sall, ya sanar da sassauta dokar hana fita ta korona ta hanyar buɗe kasuwa sau 6 a mako dare da wuraren bauta.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A dai wani bangare na nahiyar, a dai wannan ranar, masu ibada na salla tare a masallaci a karon farko bayan an sake bude masallatai a Senegal.
Zakaran gasar tsren duniya da na Olympic Mo Farah na atisaye a wajen shakatawa na Richmond, saboda barkewar cutar korona a Landan, an dauki hoton ne a ranar 12 ga watan Mayu 2020.

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Dan Somaliya kuma dan tseren Burtaniya Mo Farah na gudu da barewa a wajen shakatawa na Landan ranar Talata.
Ana yiwa wani majinyaci gwaji da ake zargin yana dauke da cutar korona a cibiyar killace marasa lafiya da ke Jami'ar maiduguri a ranar 1o ga watan Mayu 2020. - a Najeriya, kasar da ta fi kowacce yawan mutane, akwai masu korona 5,162 kuma 167 sun mutu.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A ranar Lahadi, wani ma'aikacin lafiya a Maiduguri na yi wa wani mutum gwajin cutar korona a Najeriya.
Ana yi wa wata malama gwajin korona a cibiyar lafiya ta Cadjèhoun a Cotonou a ranar 9 ga watan Mayu 2020.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Ana yi wa malamai gwajin cutar korona a Cotonou, Benin, kafin bude makarantu.
Likitocin ma'aikatar lafiya ta Kenya na daukar samfurin direbobin manyan motoci lokacin da ake musu gwajin cutar korona, a Namanga wata tsakanin Kenya da Tanzaniya, a ranar 12 Mayu 2020.

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Direbobin manyan mota da suka tsallaka daga Tanzaniya zuwa Kenya ana yi musu gwajin cutar korona a ranar Talata.
Turnikin hayaki ya baibayen saman gine-gine a babban birnin LIbya Tripoli, yayin jefa-makamai da dakarun Khalifa Haftar a ranar 9 ga watan Mayu 2020.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A ranar Asabar hayaki ya turnuke sama a babban birnin Libya Tripoli, Inda Janar Khalifa Haftar ke kaddamar da hare-harenshi kan gwamnatin da Majalisar Dinkin Duniya ke goya wa baya.

Haƙƙin mallakar hotuna: Getty/AFP/Reuters