Najeriya za ta kwaso ƴan ƙasarta 1,000 daga Afirka ta Kudu kan nuna wariya

Asalin hoton, Tinubu X
Gwamnatin Najeriya ta fara shirye-shiryen kwaso ƴan ƙasarta sama da 1,000 daga ƙasar Afirka ta Kudu a daidai lokacin da ake ƙara samun tashin-tashina da zaman ɗar-ɗar saboda nuna adawa ga baƙi da ƴa ƙasar ke yi.
Wannan yunƙurin na zuwa ne bayan ƙasar Ghana ta fara kwashe ƴan ƙasarta bayan sun fuskanci barazana daga zanga-zangar da ƴan Afirka ta Kudu ke yi, inda ake fargabar za su iya farautar baƙi ƴan ƙasashen waje.
A ranar Alhamis ne aka fara tantance ƴan Najeriya da suka nuna sha'awar komawa ƙasarsu, kamar yadda kakakin ma'aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Ebienfa ya shaida wa AFP a ranar Juma'a.
"Muna sa ran fara kwashe kusan mutum 1,000, duk da cewa ba mu da haƙiƙanin adadin waɗanda za mu kwaso. Sannan mun shiga yarjejeniya da hukumomin ƙasar kan barin waɗanda suke da matsalolin biz da suke da sha'awar ficewa a ɗaga musu ƙafa su fice maimakon a tsare su."
Ana dai fargabar farautar baƙi ne a ƙasar Afirka ta Kudu bayan wata ƙungiya ta ba ƴan ƙasashen waje wa'adin zuwa ranar 30 ga Yuni su fice daga ƙasar.


















