Buhari zai dora tubalin ginin jami'ar sufuri a Daura

An wallafa

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari zai dora tubalin ginin jam'iar sufuri wadda irin ta ce ta farko a kasar.

Ana sa ran a mako mai zuwa ne shugaban zai dora tubalin ginin a mahaifarsa da ke Daura a jihar Katsina.

Kamar yadda hukumar da ke kula da jami'oi ta Najeriya ta bayyana a shafinta na intanet, ana sa ran cewa aikin zai lashe kusan naira biliyan 18.

A wata tattaunawa da yayi da manema labarai a Abuja, Ministan Sufurin Najeriya Rotimi Amaechi ya bayyana cewa tuni aka bai wa kamfanin gine-gine na China Civil and Construction Company wato CCECC, kwangilar gina jami'ar kuma aikin zai kankama da zaran gwamnan jihar Katsina ya bayar da filin da za a gudanar da aikin.

Ministan ya bayyana cewa akwai matasa 'yan Najeriya da suka samu tallafi daga gwamnatin Najeriya domin karatu a kasar China inda suke karanta fannin aikin injiniya na jirgin kasa da layin dogo.

Ya ce da zaran sun kammala karatun, za a tura su wannan sabuwar jami'ar da za a gina ta daura su fara koyarwa kafin su kama aiki gadan-gadan.