Watakila Neymar ya buga wa Brazil wasa da Koriya ta Kudu

An wallafa

Watakila Neymar ya buga wasan da Brazil za ta fafata da Koriya ta Kudu ranar Litinin a karawar zagaye na biyu a Gasar Cin Kofin Duniya a Qatar.

Mai shekara 30 bai yi wa Brazil wasan da ta ci Switzerland ba da wanda Kamaru ta yi nasara a fafatawar cikin rukuni na bakwai.

Dan kwallon mai taka leda a Paris St Germain ya ji rauni a wasan farko a cikin rukuni da Brazil ta ci Serbia 2-0.

Brazil wadda ake sa ran za ta iya daukar kofin Qatar ta kai zaga na biyu tun kan ta fuskanci Kamaru a wasan karshe a rukuni na bakwai.

Koriya ta Kudu kuwa ta yi ta biyu ne a rukuni na takwas da maki hudu.

Wannan shi ne wasa na takwas da za a kece raini tsakanin tawagogin biyu, amma na farko a babbar Gasar tamaula ta Duniya.

Brazil ta yi nasara a wasa shida aka doke ta karawa daya - wasan karshe da suka fuskanci juna shi ne a watan Yuni, inda Brazil ta ci 5-1.

Duk wadda ta yi nasara a wasan Litinin za ta buga daf da na kusa da na karshe tsakanin Japan da Croatia.

Croatia ita ta yi ta biyu a Gasar Kofin Duniya da aka yi a Rasha a 2018, wanda Faransa ta lashe.