Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Neymar zai buga wasan Brazil da Koriya ta Kudu
An wallafa
Kocin Brazil Tite ya tabbatar da cewa Neymar zai buga wasansu da Koriya ta Kudu a zagaye na biyu na gasar cin kofin duniya da Qatar ke daukar bakunci.
Dan wasan mai shekaru 30 bai buga wasanni biyu a jere na Brazil ba, saboda raunin da ya ji a wasansu na farko da Serbiya.
Brazil wacce ake ganin za ta iya lashe gasar ta zama ta farko a rukunin G duk da cewa ta sha kashi a hannun Kamaru a wasansu na karshe na zagayen farko.
Tite ya ce "Neymar ya yi atisaye a yau kuma zai iya buga wasanmu na ranar Litinin".
Dan wasan PSG din ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa a yanzu ya samu sauki.