'An kama ɗaliban Najeriya fiye da 100 a kasar Cyprus'

'An kama ɗaliban Najeriya fiye da 100 a kasar Cyprus'
An wallafa

Ɗalibai ‘yan Najeriya sama da 100 ne ke garkame a gidajen yari daban-daban na Cyprus bayan kama su da hukumomi a kasar suka yi kan zargin sha da fataucin miyagun ƙwayoyi.

Shugaban kungiyar ɗalibai ‘yan Najeriya a Turai, Muhammad Bashiru Saidu, ya shaida wa BBC Hausa cewa gwamnatin Najeriya ta yi wa iyaye gargaɗi kan su daina tura yaransu karatu a can.

Gwamnatin Najeriya ta ce an kashe dalibai aƙalla 20 a ‘yan shekarunnan kuma babu wanda aka kama da zargin kisan ya zuwa yanzu.