Guardiola ya kara shiga matsala a wasannin da yake fuskanta

Asalin hoton, Getty Images
Manchester City ta yi rashin nasara 2-1 a hannun Manchester United a wasan mako na 16 a Premier League ranar Lahadi a Emirates.
City ce ta fara cin ƙwallo ta hannun Josko Gvardiol tun kan hutu, kuma haka suka je hutu suka koma zagaye na biyu ƙungiyar Etihad tana cin 1-0.
Sauran minti biyu a tashi daga wasan na hamayya ne, United ta farke ta hannun Bruno Fernandes, sannan Ahmad Diallo ya kara na biyu daf da za a tashi daga karawar.
Kenan City ta yi nasara ɗaya daga karawa 11 a dukkan fafatawa, wadda aka doke karo na takwas da canjaras biyu daga ciki.
Haka kuma ƙungiyar da Pep Guardiola ke jan ragama, an zura mata ƙwallo biyu a raga a karawa ta takwas daga wasa 12 a lik, fiye da yawan da suka shiga ragarta a wasa 62.
City ta haɗa maki huɗu daga fafatawa bakwai a Premier League, rashin ƙwazo mai muni da ta yi tare da Southampton a kakar nan.
Maki 27 da City take da shi bayan wasannin mako na 16, shi ne rashin kokari a irin wannan matakin tun bayan 2010.
Manchester United ce kaɗai da take da maki 27 bayan mako na 15 ta je ta lashe Premier League a kakar 2002/03.
Harry Maguire ya buga wa United wasan, kuma karo na 250 da ya yi a Premier League, wanda ya ci ƙwallo 13 ya kuma bayar da 10 aka zura a raga
Da wannan sakamakon City tana nan a mataki na biyar a teburin Premier da maki 27, ita kuwa United mai maki 22 ta yi sama zuwa mataki na 13 a gasar.











