Ku San Malamanku tare da Malam Idris Yunus Limamin masallacin Gwarimpa
Ku San Malamanku tare da Malam Idris Yunus Limamin masallacin Gwarimpa
An wallafa
Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan a Najeriya, kuma limamin masallacin Juma'a na Ƙungiyar ɗalibai ta ƙasa da ake kira Abdullateef Adegbite da ke birnin tarayyar Abuja.
Malamin, ya ce shi cikakken haifaffen Kano kuma ya yi karatu a makarantu daban-daban a jihar.
Ya ce ya yi karatun allo a wata makarantar Malan Sani da ke unguwar Birdget, daga nan ya koma karatu wajen marigayi Malam Mahmoud Ilyasu Dokoki, kuma shi ne wanda ya fi tasiruwantuwa d karatunsa.



