Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Dan wasan Faransa, Mbeumo ya koma buga wa Kamaru
Dan wasan gaba na Brentford Bryan Mbeumo ya sauya sheka daga buga wa Faransa wasa zuwa Kamaru.
An haifi Mbeumo, wanda a ranar Lahadi zai cika shekara 23, a Avallon da ke tsakiyar Faransa.
Ya taka wa Faransar leda a tawagar 'yan kasa da shekara 20 da kuma ta 'yan kasa da shekara 21, amma kuma ya cancanci buga wa kasar mahaifinsa, Kamaru wasa.
A wani sakon tuwita da ya sanya ya nuna irin dokin da yake cike da shi na taka wa Kamaru leda.
Hukumar kwallon kafa ta Kamaru (Fecafoot) ta ce shawarar da Mbeumo ya yanke ta komawa yi wa Kamaru wasa ta kasance ne sakamakon tattaunawa da shugaban hukumar Samuel Eto'o, ya tsananta da shi.
Yanzu sai Fecafoot ta samu takarda daga Fifa, wadda za ta ba dan wasan damar yi wa Kamaru wasa saboda ya yi wa Faransa wasa har sau 10 a matakin matasa.
Hukumar ta kamaru ta ce tana da kwarin guiwa za ta samu wannan takardar izini da ta za ta ba shi damar buga wa tawagarta a gasar kofin duniya da za a yi a a Qatar nan gaba a shekaran nan.
Kamaru na rukuni daya da Brazil da Serbia da kuma Switzerland a rukuni na 7, wato Group G a gasar ta duniya.
Mbeumo, wanda mahaifiyarsa 'yar Faransa ce ya fara sanar kwalon kafa a kungiyar Troyes ta Faransa kafin ya tafi Brentford, a lokacin tana gasar kasa da Premier wato Championship, a watan Agusta na 2019.
Ya ci kwallo 16 a wasan lig 45 a kakarsa ta farko kafin daga baya kuma ya kara 8 a kakar 2020-21 inda ya taimaka wa kungiyar hawa gasar Premier.
Dan wasan ya zura kwallo 8 a wasa 38 a dukkanin wasannin da ya yi wa kungiyar a bara, tare da bayar da kwallo a ci sau 7 a Premier, yayin da Brentford ta kammala kakarta ta farko a matsayi na 13.
Yana da kwantiragi da kungiyar ta yammacin London har zuwa shekara ta 2026.