Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
'Abin da ya sa nake son zama gwamnan Jihar Zamfara'
Dan takarar gwamnan Jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya a jam'iyyar African Democratic Congress, ADC, Ahmad Hashim Tsani, ya ce rashin sanya mutane ciki shirin ci gaban jihar shi ya sa take fuskantar koma-baya a dukkan bangarorin rayuwa.
Ya bayyana haka ne a tattaunawa ta musamman da BBC Hausa.
"Ci gaba mai dorewa ya yi karanci a Jihar Zamfara saboda ba a dauki al'ummomi an sanya su a gaba ba. Duk wani ci gaba da za a kawo ya kamata a ce jama'a ne a gaba," in ji shi.
Ya ce zai mayar da hankali wajen magance matsalolin da suke addabar jihar, kasancewarsa wanda ya yi rayuwarsa gaba daya a cikin jihar.