'Abin da ya sa nake son zama gwamnan Jihar Zamfara'

Bayanan bidiyo, Danna hoton da ke sama domin kallon bidiyon:
'Abin da ya sa nake son zama gwamnan Jihar Zamfara'
An wallafa

Dan takarar gwamnan Jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya a jam'iyyar African Democratic Congress, ADC, Ahmad Hashim Tsani, ya ce rashin sanya mutane ciki shirin ci gaban jihar shi ya sa take fuskantar koma-baya a dukkan bangarorin rayuwa.

Ya bayyana haka ne a tattaunawa ta musamman da BBC Hausa.

"Ci gaba mai dorewa ya yi karanci a Jihar Zamfara saboda ba a dauki al'ummomi an sanya su a gaba ba. Duk wani ci gaba da za a kawo ya kamata a ce jama'a ne a gaba," in ji shi.

Ya ce zai mayar da hankali wajen magance matsalolin da suke addabar jihar, kasancewarsa wanda ya yi rayuwarsa gaba daya a cikin jihar.