Ku San Malamanku tare da Sheikh Abdulƙadir Saleh Kazaure

Bayanan bidiyo, Dannan hoton nan domin kallon bidiyon
Ku San Malamanku tare da Sheikh Abdulƙadir Saleh Kazaure
An wallafa

A wannan makon filinmu na Ku San Malamanku ya tattauna da Sheikh Abdulƙadir Saleh Kazaure da ke garin Kazauren jihar Jigawa a Najeriya.

Malamin ya shaida wa BBC Hausa cewa an haife shi a unguwar Lokon Rijiya cikin garin Kazaure a 1972.

Malamin ya fara karantunsa na boko a Makarantar Kudu Firamare, kafin a kai shi karatun allo yana ɗan shekara bakwai a tsangayar Balbela cikin birnin Maiduguri.

Ya shiga Fitacciyar Sakandiren SAS ta Kano, kuma bayan ya kammala ne ya tafi Kwalejin Nazarin Shari'a da Al'amuran Addinin Musulunci ta LEGAL da ke Kano. Ya yi karatu a ƙarƙashin fitaccen malamin nan, Sheikh Jaafar Mahmud Adam. Ya kuma samu tallafin karatu a ƙarƙashin Cibiyar Al-Muntadah, sannan ya tafi Sudan inda ya kammala karatun digirinsa na 2 a shekara ta 2013.