Zanga-zanga na neman mamaye titunan ƙasar Peru

..

Asalin hoton, Reuters

An wallafa

Fusatattun magoya bayan shugaban Peru da aka tsige mai sassaucin ra'ayi Pedro Castiyo sun yi arangama da jami'an tsaro a daidai lokacin da zanga-zanga ta kacame a faɗin ƙasar.

Aƙalla mutum mutum biyu suka rasu a lardin Apurimac da ke kudancin ƙasar, haka kuma jama'a da dama sun raunata sakamakon tarzomar da ta kunno kai. A ranar Laraba ne Majalisar Dokokin ƙasar ta tsige Mista Castiyo bayan shafe watanni 16 kacal kan mulki.

A halin yanzu Mista Castiyo wanda ake zargi da cin hanci da kuma ƙoƙarin rushe majalisar dokokin ƙasar na garƙame a hannun ƴan sandan na Peru.

Magoya bayansa sun ce zarge-zargen da ake yi masa, masu ƙarfin faɗa a-ji a ƙasar ne kawai suka ƙiƙire su saboda irin rawar jikin da suke yi ta karɓar mulki.

Haka kuma an ci gaba da irin wannan zanga-zanga a babban birnin ƙasar wato Lima.

Ƴan sanda sun harba hayaƙi mai sa hawaye a ranar Lahadi domin tarwatsa masu zanga-zanga a birnin.

Haka kuma masu zanga-zangar sun yi wa 'yan sanda hamsin da wasu ma'aikatan gwamnati kawanya a filin jirgin saman Andahuaylas.

Hotunan da ake yadawa a shafukan sada zumunta na nuna hayaki na tashi a filin jirgin saman, wanda ke kudancin kasar.

Hukumar da ke kula da sufurin jirgin sama ta kasar CORPAC ta ce an lalata wasu bangarori - kuma an cinna wa gine-gine wuta a filin jirgin saman - a sanadiyyar barkewar mummunar zanga-zangar.