Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Ku San Malamanku tare da Malam Usman Nagoda
Ku San Malamanku tare da Malam Usman Nagoda
An wallafa
A wannan mako, shirinmu na Ku San Malamanku ya tattauna da malamin addinin Musulunci Malam Usman Nagoda da ke birnin Kano.
An haifi malamin ne a birnin na Kano cikin 1977.
Ya fara karatun allo ne a wurin kakansa, Malam Danjuma Mai Tosaro.
Malamin ya ce daga nan ne ya shiga makarantar firamare ta Magwan, kuma bayan ya kammala ya tafi Sakandire a Kazaure.
Ko da yake, ya koma makarantar Sakandire ta Gwale a birnin Kano inda ya kammala karatu.
Ku kallo bidiyon da ke sama don sauraren cikakken tarihin malamin: