Ku San Malamanku tare da Gwana Aisha Gwani Yahuza Ɗanzarga
Ku San Malamanku tare da Gwana Aisha Gwani Yahuza Ɗanzarga
An wallafa
Aisha Yahuza Ɗanzarga - wadda ake yi wa laƙabi da Maraƙisiyya - na ɗaya daga cikin mata da aka fara naɗawa a matsayin gwanayen Alƙur'ani a ƙasar Hausa.
Mahaifinta Gwani Yahuza Danzarga shahararren malamin Ƙur'ani ne a jihar Kano da ke arewacin Najeriya, kuma shi ne ya naɗa ta gwana.
Ta taɓa wakiltar Najeriya a musabaƙar Ƙur'ani ta duniya da aka yi a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (Dubai), inda ta zo ta biyu a ajin hizifi 60.
Haifaffiyar birnin Kano ce kuma a nan ta yi karatun littafin mai tsarki da na zamani.



