Ku San Malamanku tare da Gwana Aisha Gwani Yahuza Ɗanzarga

Bayanan bidiyo, Latsa hoton sama ku kalli bidiyo:
Ku San Malamanku tare da Gwana Aisha Gwani Yahuza Ɗanzarga
An wallafa

Aisha Yahuza Ɗanzarga - wadda ake yi wa laƙabi da Maraƙisiyya - na ɗaya daga cikin mata da aka fara naɗawa a matsayin gwanayen Alƙur'ani a ƙasar Hausa.

Mahaifinta Gwani Yahuza Danzarga shahararren malamin Ƙur'ani ne a jihar Kano da ke arewacin Najeriya, kuma shi ne ya naɗa ta gwana.

Ta taɓa wakiltar Najeriya a musabaƙar Ƙur'ani ta duniya da aka yi a ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (Dubai), inda ta zo ta biyu a ajin hizifi 60.

Haifaffiyar birnin Kano ce kuma a nan ta yi karatun littafin mai tsarki da na zamani.