Wataƙila Jorginho ya koma taka leda a kakar bana bayan jinyar huhu

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Kocin Arsenal Mikel Arteta ya ce ɗanwasansa na tsakiya Jorginho yana "samun sauƙi" daga jinyar huhu, inda ya ce da alama ɗanwasan zai iya komawa taka leda a kakar bana.

Wasan ƙarshe da ɗanwasan mai shekara 33 ya taka shi ne a 12 ga Afrilu, amma aka cire shi a ƙarshen wasan, wanda ƙungiyar ta yi kunnen-doki da Brentford saboda zafi da yake ji a ƙirginsa.

Da yake jawabi a game da wasan ƙungiyar na Premier na ranar Asabar da za su fafata da Bournemouth, Arteta ya ce: "Yana samun sauƙi."

Arsenal ba ta tabbatar da irin jinyar da yake yi ba, amma wata majiya ta ce ya ji ciwo ne a huhunsa.

A game da yiwuwar mataimakin kyaftin ya taka wasa a kakar bana, Arteta ya ce: "ina tunanin idan komai ya fi daidai, zai dawo taka leda a wasu makonni a nan gaba."

Jorginho na gab da ƙarshen kwantiraginsa a Arsenal, inda ake tunanin zai bar ƙungiyar kafin kakar baɗi.

Ɗanwasan ɗan asalin ƙasar Italiya ya buga wasa 78 tun zuwansa ƙungiyar daga Chelsea a Janairun 2023 a kan fam miliyan 12.

Shi ma Kai Havertz akwai alamar zai koma taka leda a kakar bana bayan jinyar da yake yi.