Ku San Malamanku tare da Sheikh Dan'azumi Musa Tafawa Ɓalewa

Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon
Ku San Malamanku tare da Sheikh Dan'azumi Musa Tafawa Ɓalewa
An wallafa

A shirin Ku San Malamanku na wannan mako, mun gabatar muku da Sheikh Dan'azumi Musa Tafawa Ɓalewa.

An haifi shehin malamin a 1953, a Tafawa Balewa da ke jihar Bauchi, ya fara karatun Ƙur'ani tun yana da shekara uku tun a gidansu.

Sannan ya shiga makarantar boko a garin Tafawa Ɓalewa, tun yana da shekara tara zuwa 10.

Bayan kammala furamare ya tafi garin Kano inda ya shiga makarantar sakandire a makarantar Sheikh Nasiru Kabara a Shahuci a birnin Kano.

Malamin ya yi digirinsa na farko a fannin Tarihi da addinin musulunci da kuma harshen Larabci a jami'ar Bayero ta Kano.

Ya kuma yi digirinsa na biyu a jami'ar Jos da ke jihar Plateau, yanzu haka kuma yana karatun diginsa na uku a jami'ar jihar Benue.

Manyan malaman da ya yi karatu a wajensu sun haɗa da Sheikh Nasiru Kabara da Sheikh Dahiru Bauchi da sheikh Ali tsafe.

Malamin ya ce ya je ƙasashe Irin Masar da Iraƙi da Senegal duk a harkokin karutun addini.

A yanzu haka Sheikh Dan'azumi shi ne shugaban majalisar Malamai ta ƙasa reshen jihar Bauchi, kuma mataimakin shugaban majalisar malamai ta ƙasar, kamar yadda ya bayyana.