Zan fi bai wa fannin ilimi muhimmanci a jihar Yobe - Dan takarar PDP
Zan fi bai wa fannin ilimi muhimmanci a jihar Yobe - Dan takarar PDP
An wallafa
Dan takarar kujerar gwamna na jihar Yobe, a jam'iyyar adawa ta PDP, Alhaji Sharif Abdullahi ya ce burinsa shi ne ganin fannin ilimi ya habaka.
A cewarsa " jihar Yobe na fuskantar matsaloli da dama amma babu kamar matsalar raunin fannin ilimi kasancewar ita ce ta haifar da duk matsalar da jihar ke ciki a yanzu haka."



