Cutar murar aladu ta hallaka dalibai a Ghana

Asalin hoton, Getty Images
An wallafa
Hukumomin lafiya a Ghana sun tabbatar da cewar cutar murar aladu itace ta yi sanadiyyar mutuwar wasu dalibai hudu a babbar makarantar sakandire ta Kumasi Academy.
Sun kuma ce ana jinyar wasu daliban a wasu asibitoci da ke Kumasi.
A gwaje -gwajen farko da aka yi, an kasa gano cewa cutar ce tayi sanadiyyar mutuwar daliban amma daga bisani an tabbatar da bullar cutar.
Wakilin BBC da kai ziyara yankin ya ce dalibai kalilan ne suka rage a makarantar saboda iyaye sun kwashe 'yayansu daga makaratar.
An kuma dage taron iyayen yara da aka aka shirya yi a ranar Asabar zuwa ranar Litinin.
Sai dai kawo yanzu dai hukumomi na cigaba da bayar da rigakafi ga daliabai da sauran ma`aikatan makarantar.

Asalin hoton, Getty Images







