Champions League: Frank Lampard yace yana da yakinin zasu samu galaba a kan Valencia

An wallafa

Kocin Chelsea Frank Lampard ya ce wasan su da zasu yi da Valencia a gasar Zakarun Turai na nufin ba zasuyi rashin nasara ba, ko da kuwa ba su samu abinda suke so ba.

Chelsea dai na mataki na biyu a saman teburin rukuni na takwas. Abinda take nema shine samun nasara a wasan domin tsallakawa zagaye na 16.

Kungiyar dai ta sha kaye da ci 1-0 har gida a hannun Valencia a zagayen farko na wasan rukuni.

Amma Lampard ya ce kayen da suka sha ne ya sanya suka shiga matakin da suke a saman teburi.

"Tawagarmu tana da kyau, sai dai ka yi wasarere da aikin ka to kuwa zaka gani a kasa. kuma abinda muke fuskanta kenan a halin yanzu", inji Lampard.

"Munyi kuskure sosai, amma zamu gyara."

Kungiyar zata yi wasanta ba tare da da wasa Callum Hudson-Odoi ba, kuma 'yan wasa irin su Ross Barkley da Antonio Rudiger basa cikin tawagar da zasu fafata a wasan nata da Valencia, duk da cewa sun fito a filin atisaye.

A wani labarin kuma, kocin Valencia Albert Celades ya ce kungiyar da zasu karbi bakuncinta na daya daga cikin manyan kungiyoyi da ke turai, don haka akwai aiki a gabansu.

Chelsea ta samu nasara a wasanninta 13 da tayi a dukkanin gasar da ta fito, ko da yake ta sha kaye a hannun Manchester City a wasansu da suka yi tattaki a gasar Premier.

Dukkanin kungiyoyin biyu na da maki bakwai a saman teburi tare da Ajax. Kuma kowannen su nasara yake nema a wasan da zai yi.