Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Riyad Mahrez ya koma Man City
An wallafa
Kungiyar Manchester City ta sayi dan wasan Leicester City Riyad Mahrez a kan fam miliyan 60.
Dan kwallon mai shekara 27 shi ne dan wasan farko da City ta saya tun bayan lashe Gasar Firimiya ta bana.
Tun a watan Janairun City ta so sayen dan wasan, amma sai cinikin bai kammalu ba.
Mahrez, wanda dan kasar Aljeriya ne, ya koma Leicester City ne daga kungiyar Le Havre a kan fam 400,000 a shekarar 2014.
Ya ci wa Leicester kwallaye 48 a wasanni 179 da ya taka mata leda.
Karanta wadansu karin labarai