Jesus ne matashin dan kwallo mafi kwazo bayan Messi

An wallafa

Gabriel Jesus wanda ya ci kwallo biyu a wasan da suka buga da Stoke, "shi ne matashin dan kwallo mafi kwazo wanda ba a samu kamarsa ba tun bayan Messi, in ji Danny Murphy.

Tsohon dan wasan Ingila, Murphy, ya shaida wa BBC cewa bayan Lionel Messi, bai sake ganin wani matashin dan kwallo da ke taka leda kamar Jesus ba.

Manchester City ce kungiyar da take samun tagomashi kawo yanzu a bana, inda ta zazzaga wa Stoke kwallo bakwai a karawar da suka yi.

Kuma ita ce kungiyar da take jan ragama a teburin firimiya a yanzu inda ta bai wa Manchester United tazarar maki biyu.

Kawo yanzu City ta ci kwallo 29 a cikin mako takwas na fara wasan kakar bana, rabon da a samu irin wannan tun wasan da Everton ta yi a kakar 1894-95.

Gabriel Jesus, dan kasar Brazil, na haskakawa sosai tun bayan da ya koma City a kakar bara.

Tuni ya ci kwallo bakwai a wasa 11 da ya bugawa kasar.

A yauzu dai za a zuba ido a ga irin rawar da zai taka nan gaba a rayuwarsa, domin taka sahun Messi a fagen tamola ba karamin aiki ba ne.