Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Gane Mini Hanya: Gwamna Matawalle ya gabatar da buƙatun Zamfara a taron sauyin yanayi
Latsa hoton sama ku saurari Shirin Gane Mini Hanya
A ranar Juma'a ne aka kawo karshen taron Majalisar Dinkin Duniya (MDD) kan sauyin yanayi a birnin Glasgow na Birtaniya.
Gwamnatoci da kwararru ne suka hadu domin samun mafita game da yadda duniya ke kara dumama da nufin samo hanyoyin warware matsalolin.
Gwamnan Jihar Zamfara a Najeriya, Bello Muhammad Matawalle, shi ma ya halarci wannan taro, inda ya gabatar da bukatun jiharsa.
A cikin wata hira da Ahmad Abba Abdullahi, ya fara ne da yi masa bayani kan abubuwan da ya gabatar a wajen taron, kafin su tattauna kan kalubalen tsaron da jiharsa ke fuskanta.