Gane Mini Hanya: Gwamna Matawalle ya gabatar da buƙatun Zamfara a taron sauyin yanayi

An wallafa

Latsa hoton sama ku saurari Shirin Gane Mini Hanya

A ranar Juma'a ne aka kawo karshen taron Majalisar Dinkin Duniya (MDD) kan sauyin yanayi a birnin Glasgow na Birtaniya.

Gwamnatoci da kwararru ne suka hadu domin samun mafita game da yadda duniya ke kara dumama da nufin samo hanyoyin warware matsalolin. 

Gwamnan Jihar Zamfara a Najeriya, Bello Muhammad Matawalle, shi ma ya halarci wannan taro, inda ya gabatar da bukatun jiharsa. 

A cikin wata hira da Ahmad Abba Abdullahi, ya fara ne da yi masa bayani kan abubuwan da ya gabatar a wajen taron, kafin su tattauna kan kalubalen tsaron da jiharsa ke fuskanta.