Shirin ci-rani a Jamhuriyar Nijar na 22/08/2021
An wallafa
Latsa hoton sama ku saurari shirin Ci-ranin mutanen Tahoua na Jamhuriyyar Nijar a madadin Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu
A cikin shirinmu na musamman kan ci-ranin mutanen Tahoua na Jamhuriyyar Nijar kashi na 14, AbdusSalam Ibrahim Ahmed ya ɗora daga inda ya tsaya a makon da ya gabata.
A wannan karon, ya tattauna ne da mazan da suke tafiya ci-rani da irin kalubalen da suke fuskanta.
Shirin na zuwa muku ne a madadin filin Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu.