Ana fargaba kan makomar mutanen da suka makale a mahakar ma'adinan a Burkina Faso
An wallafa
Danna hoton da ke sama domin kallon bidiyon:
Ana ci gaba da neman ma'aikatan hakar ma'adinai takwas da suka makale a karkashin kasa tsawon makonni hudu a wani wajen hakar ma'adanin zinc da ke Burkina Faso.
'Yan kasar Burkina Faso shida da dan Zambia daya da kuma dan kasar Tanzania sun makale a karkashin kasa bayan wani mamakon ruwan sama ya mamaye wurin hakar ma'adinai na kamfanin Perkoa na kasar Canada.
Wakiliyar BBC Lalla Sy ta hada mana wannan rahoton: