Bidiyon Ku San Malamanku tare da Sheikh Usman Isa Taliyawa

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

Malamin addinin Musuluncin nan na Gombe Sheikh Usman Isa Taliyawa ya ce su suka soma kafa Fitiyanul Islam a Kano zuwa Gombe, karkashin jagorancin Modi Salga da Aliyi Alkali.

Sheikh Usman Taliyawa wanda ya shafe tsawon shekaru yana koyarwa da da'awa ya ce ba shi da wani buri a yanzu ganin ya rabu da duniya cikin imani da rufin asiri.

Malamin wanda shi ne mataimakin Bala Lau shugaban kungiyar Izala ya shaida haka ne a shirin Ku San Malamanku na BBC.