Atiku Abubakar: Ƴan Najeriya ne ke son na tsaya takara a 2023

Bayanan bidiyo, Atiku Abubakar
An wallafa

Latsa hoton sama domin kallon bidiyon

Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya Alhaji Atiku Abukabar ya ce ƴan kasar ne suka buƙaci ya tsaya takarar shugaban ƙasa a shekarar 2023.

Atiku ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a Abuja ranar Talata kwana guda kafin ya ayyana takararsa a hukumance.