Bidiyon Ku San Malamanku tare da Malam Ibrahim Mustapha Malik

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

Fitaccen malamin addinin musulunci a jihar Borno arewa maso gabashin Najeriya Malam Ibrahim Mustapha Malik ya ce ya samu karatun addini a ƙasar Saudiyya kuma ya yi karatun boko har zuwa digiri na biyu.

Malamin ya ce yana cikin manyan almajiran Sheikh Abba Aji fitaccen malamin addinin musulunci a jihar Borno.

Ya ce ya yi karatun litattafai da dama wurin malaminsa Shekih Abba aji.