Bidiyon Ku San Malamanku tare da Sheikh Muhammad Tukur Jangebe

Bayanan bidiyo, Ku San Malamanku tare da Sheikh Muhammad Tukur Jangebe
An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

An haifi Malam Muhammad Tukur Sani Jangebe a garin Jangebe a ranar 26 ga watan Oktoba 1959, a masarautar Talatar Mafara da ke jihar Zamfara.

Ya fara karatun Alkur'ani a wajen kanin mahaifinsa Malam Muhammadu Ana Ruwa, daga nan zuwa ga kakansa Malam Alhassan a garin Gusau.

Amma inda ya yi karatu mai zurfi, shi ne a wajen Malam Abdurrahman Malam Ango Kalgawa a garin Gulma, inda ya shekara bakwai a hannunsa.

A nan ya koyi daukacin karatun Alkur'ani da rubuta shi da sauke shi, daga baya ya ci gaba da karatun littafan musulunci daga garin Gulma zuwa Sakkwato, da Zaria ya kuma dangana ga marigayi Sheikh Abubakar Gumi a jihar Kaduna.