Ku San Malamanku tare da Sheikh Jalo Jalingo

Bayanan bidiyo, Ku San Malamanku tare da Sheikh Jalo Jalingo
An wallafa

Latsa hoton sama ku kalli bidiyo

Shahararren malamin Musuluncin nan, Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Muhammad Jalingo ya ce ya fara karatu ne domin ya ƙware a harshen Larabci da kuma adabi ba wai karatun Fiƙihu da sauransu ba kafin daga baya ƙaddara ta sauya masa layi.

An haifi malamin a garin Jacci da ke Jihar Taraba a arewa ta tsakiyar Najeriya a shekarar 1960.