Bidiyon Ku San Malamanku tare da Sheikh Abdulwadud Harun Attijjaniy

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

A cikin shirinmu na Ku San Malamanku na wannan makon, a wannan makon mun tattauna da shugaban gudanarwar darikar Tijjaniyya a kasar Ghana Sheiekh Abdulwadud Harun Attijjaniy

Malamin ya bayyana cewa an haife shi a darikar Tijjaniyya ya kuma taso a cikinta, sannan ya yi rubuce-rubuce a kanta.

Ya ce ya shiga kauyuka da birane domin yada addinin Musulunci da darikar ta Tijjaniyya.

Sheikh Harun ya ce a Ghana akwai fahimtar juna tsakanin kungiyoyin Musulmin kasar, haka kuma suna zaman lafiya da mabiya wasu addinan.