Abdulaziz Yari: Za mu sake kafa gwamnati a jihar Zamfara a 2023

An wallafa

Latsa hoton sama domin kallon hirar

Tsohon gwamnan Zamfara Abdul'aziz Yari Abubakar ya ce APC ta sasanta da ɓangarorinta da ke rikici domin kafa gwamnati a 2023.

A hirarsa da BBC ya ce yanzu an fahimci juna tsakaninsa da bangarorin Jam'iyyar APC da ke rikici kuma sun yadda kaddara ce ta fada wa jam'iyyar a zaɓen 2019.

Rikicin jam'iyyar APC a Zamfara ne ya sa Jam'iyyar PDP ta tsinci dami a kala sakamakon hukuncin kotun koli da ya soke dukkanin kujerun da jam'iyyar APC ta lashe a jihar a zaben 2019.