Bidiyon Ku San Malamanku tare da Dokta Zakariyya Sa'id Zakariyya

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

An haifi Dokta Zakariyya a shekarar 1960, a wata tsangaya dake Kandi a karamar hukumar Dutse ta jihar Jigawa.

Mahaifinsa Malami ne na Alkur’ani wanda yake da almajirai da dama.

Dokta Sa’idu ya shafe shekaru yana karatun Alkur’ani a gidansu, kafin daga baya ya tafi garuruwa da dama da suka hada da Takai a jihar Kano da garin Bauchi da birnin Kano da biranen Zariya da Kaduna a jihar Kaduna.