Bidiyon Ku San Malamanku tare da Sheikh Nur Arzai

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

Ɗaya daga cikin fitattun malaman addinin Musulunci a Jihar Kano da ke arewacin Najeriya Sheikh Muhammad Nur Muhammad Arzai, ya ce babu abin da ya fi farin ciki da shi a rayuwarsa fiye da kasancewarsa shi da ƴaƴansa har da wasu jikokinsa koyarwa suke yi.

Sheikh Nur Arzai shi ne limamin Masallacin Juma'a na Sunusi Dantata da ke Kofar Ruwa a Kano, ya ce ya buɗe makarantu da dama musamman don koyar da yara ƙanana, kuma a yanzu ma yana da burin buɗe wasu ƙarin makarantun a wasu jihohin Najeriya inda za a ringa karantar da yara addinin Musulunci.

Sheikh Nur Arzai wanda yana ɗaya daga cikin manyan jigogin ɗariƙar Tijjaniya a Kano, ya bayyana haka ne a cikin shirin Kusan Malamanku na BBC Hausa, lokacin da yake bayani kan iyalensa.

Ɗaukar bidiyo da tacewa: Yusuf Ibrahim Yakasai