Cinikayyar kasuwar 'yan wasan tamaula ta bana

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kan cefanen 'yan kwallo da labarin wasanni.

Rahoto kai-tsaye

  1. AC Milan na zawarcin Okafor

    ...

    Asalin hoton, NOAH.ARINZE/INSTAGRAM

    AC Milan na daf da kulla yarjejeniya da Red Bull Salzburg kan Noah Okafor daga Salzburg, a cewar wani rahoto.

    An sami labarin cewa Milan na gab da kulla yarjejeniya da Salzburg don siyan Okafor, kuma har kungiyar ta shirya gwajin lafiya da za a gudanar ranar Asabar a lokacin lokacin da dan wasan zai sauka a Milan, idan komai ya tafi yadda ya kamata.

    An dade da tabbatar da cewa dan wasan kasar Switzerland ya riga ya amince yarjejeniya tsakaninsa da Rossoneri kuma yana cikin jerin sunayen Stefano Pioli na wadanda za su bugawa kungiyar a kaka mai zuwa, in ji dan jaridar.

    Dan wasan mai shekaru 23, ya buga wa Salzburg wasanni 110, inda ya zura kwallaye 34 a raga kuma ya taimaka aka zura kwallaye 23 a wannan lokacin.

    Ya zura kwallo a ragar Milan a gasar cin kofin zakarun Turai da aka buga a bara a Salzburg, wanda ya ba ta damar ci 1-0.

    Ya buga mafi yawan wasanni a matsayin dan wasan gaba. Ya buga wasanni 60 a matsayin dan wasan gaba, inda ya zura kwallaye 23 sannan ya taimaka sau 15.

  2. An umarci dan wasan Senegal ya biya Watford fan miliyan 2.3 a matsayin diyya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An umarci dan wasan Senegal Pape Gueye da kuma kungiyar kwallon kafa ta Marseille na Faransa da cewa dole su biya Watford fam miliyan 2.3 kan karya kwantiragin da aka yi a shekarar 2020.

    Kotun sauraren kararrakin wasanni (Cas) ta sanar a ranar Juma’a cewa ta amince da takunkumin da hukumar kwallon kafa ta duniya (FIFA) ta kakaba a baya.

    Gueye, mai shekaru 24, wanda ya buga wasanni 74 a gasar Ligue 1, an yanke masa hukuncin dakatarwa na tsawon watanni hudu daga buga kwallo. Amma Cas ya soke haramcin sayan 'yan wasa na shekara guda da aka sanya wa Marseille.

    Rikicin ya fara ne a cikin 2020, lokacin da Gueye ya sanya hannu kan yarjejeniyar da kungiyar Watford da ke premier League a wannan lokacin, a watan Afrilu - kuma ita kungiyar ta sanar da sabon dan wasanta daga Le Havre.

    Amma dan wasan daga baya ya janye daga ya koma Marseille ta Ligue 1 a watan Yuli kan kwantiragin shekaru hudu.

    A watan Janairun 2022, Fifa ta dakatar da Gueye na tsawon watanni hudu tare da biyan tara- hukuncin da Gueye da Marseille da Watford suka kalubalanta a Cas.

    Cas ta ce yakamata Gueye da Marseille su biya tarar tare.

    Gueye ya bayar da hujjar cewa wakilinsa ne ya ba shi mugunyar shawara kan albashin da zai iya karba daga Watford.

  3. Watford ta dauki Livermore kan gajeren kwantaragi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Watford ta sayi tsohon dan wasan Ingila Jake Livermore.

    Dan wasan mai shekaru 33, wanda ya zo watford ne a kyauta bayan ya bar West Bromwich Albion, a halin yanzu yana atisaye da Hornets kuma ya sanya hannu kan kwantiragin shekara daya.

    Livermore ya shafe shekaru shida da rabi tare da Albion, inda ya buga wasanni 206 ciki har da 17 a bara.

    Ya fara wasa a Tottenham Hotspur, wadda ta sayar da shi ga Hull City a 2014 bayan ya fara zuwa a matsayin aro.

    Wasansa na karshe a cikin wasanni bakwai da ya buga wa Ingila ya zo ne a kunnen doki da Ingila ta yi da Brazil a watan Nuwamban 2017.

  4. Aubameyang ya koma Marseille

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Marseille ta sanar da daukar dan wasan gaba na Chelsea, Pierre-Emerick Aubameyang.

    Dan wasan gaban Gabon, mai shekaru 34, ya ci kwallaye uku kacal a wasanni 22 da ya buga wa Chelsea, bayan zuwansa daga Barcelona kan kudi fan miliyan 10.3 a watan Satumbar da ta gabata.

    Ba a sami tabbacin ko Marseille ta biya chelsea kudin sayen tsohon kyaftin din Arsenal din ba.

    Aubameyang ya fice daga gasar Premier a karo na biyu cikin watanni 18, bayan ya shafe shekaru hudu a Arsenal daga 2018 kafin ya koma Barca a watan Janairun 2022.

    Ya zura kwallaye 13 a wasanni 23 a cikin watanni shida da ya yi a Spain, amma ya kasa yin irin wannan salon a karkashin kociyoyi uku daban-daban a tsawon kakar wasa a Stamford Bridge.

    Gwarzon dan kwallon Afrika na shekarar 2015 ya zo ne a karshen kasuwar cinikin 'yan wasa ta bazara kuma ya buga wasa daya kacal a karkashin Thomas Tuchel, tsohon kocinsa a Borussia Dortmund, kafin a kori Bajamushen, aka maye gurbinsa da Graham Potter.

  5. Ac Milan na shirin daukan Chukwueze

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An sami rahotannin cewa Ac Milan ta kusa kammala sayuen dan wasn Najeriya Samuel Chukweze daga Villareal.

    Bayan kammala yarjejeniyar da za ta kawo Noah Okafor zuwa Milan daga Salzburg, Calciomercato ta ruwaito cewa yanzu haka Chukwueze ya shirya tsallakawa zuwa filin wasan San siro bayan wata sabuwar tattaunawa tsakanin mahukuntan Milan da takwarorinsu na Villarreal a yau.

    An sami labarin cewa an kusa cimma yarjejeniya kan Yuro miliyan 25 a matsayin kayyadadden kudin da za a biya da kuma kari da za su kai €28m gaba daya, kuma an riga shiryawa dan wasan kwantiragin shekara biyar.

    Bayanen karshe ne kawai su ka rage, amma ana sa ran za a iya kammala cinikin a karshen makon nan..

  6. Gasar cin kofin duniya: Ingila ba ta shakkan kowa- Millie Bright

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Tawagar kwallon kafan mata na kasar Ingila a shirye ta ke don tunkarar kowa a filin wasa a gasar cin kofin duniya na mata da ke gudana a Australiya da NewZealand.

    Kyaftin din 'yan wasan Millie Bright ta bayyana haka yayin da Ingila ke shirin buga wasan ta na farko a gasar inda za ta fafata da kasar Haiti ranan Asabar, a filin wasa na Brisbane.

    Bright ta yi ikirarin cewa 'yan wasan ba su shakkan fafatawa da kowa a gasan.

    Ingila na neman lashe gasar cin kofin duniya ta mata na farko yayin da wannan shi ne karin farko da Haiti ke buga gasar.

    Bayan wasansu da Haiti Ingila za su yi wasa da Denmark da kuma China.

    Ingila wacce ke matsayi na hudu a duniya na daya daga cikin kasashen da ake ganin za su iya lashe gasar amma tana fuskantar kalubale mai tsanani daga Amurka, wadanda ke da burin zama kasa ta farko da ta lashe kofuna uku a jere.

  7. Shahararren dan dambe ya rattaba hannu kan kwantiragi da kungiyar kwallon kafa

    ...

    Asalin hoton, FC Polissia

    Zakaran damben duniya a matakin masu nauyi na WBO da WBA da IBF Oleksandr Usyk ya rattaba hannu kan yarjejeniyar kwallon kafa da kungiyar kwallon kafa ta FC Polissia ta Ukraine.

    Dan wasan mai shekaru 36 ya buga wasa daya inda ya shigo daga baya a wata wasan sada zumunci a bara kuma zai saka riga mai lamba 17.

    Duk da haka, abin bakin ciki ga magoya bayan Polissia kasancewarsa zakaran damben duniya abin da zai kasance kan gaba ke nan a bubuwan da zai bai wa muhimmanci saboda haka ba kasafai ne za su gan shi a filin wasa ba.

  8. Newcastle na sa ran dauko Livramento

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Newcastle United na gab da kulla yarjejeniya da dan wasan baya na Southampton Tino Livramento.

    Kocin Magpies Eddie Howe ya kai wa dan wasan na Ingila 'yan kasa da shekara 21 hari, yayin da ake ci gaba da neman cimma yarjejeniya, BBC Sport ta fahimci cewa tattaunawar tana tafiya yadda ya kamata, tare da kyautata zaton Livramento zai kare a St James' Park.

    Ana dai fatan Livramento zai zama dan wasa na biyu da Magpies suka dauko cikin 'yan kwanaki bayan da aka cimma yarjejeniya da Leicester City kan dan wasan gefe Harvey Barnes, wanda ake tunanin farashinsa zai kai kusan fam miliyan 38.

  9. Babu yarjejeniya da Man City kan Gvardiol, in ji RB Leipzig

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Daraktan wasanni na RB Leipzig Max Eberl ya ce "babu yarjejeniya" tsakanin kulob din ta Jamus da Manchester City kan dan wasan bayan Croatia Josko Gvardiol.

    Dan wasan mai shekaru 21 yana da darajar fan miliyan 86 kuma idan City ta biya kudin hakan zai sa ya zama dan wasan baya mafi tsada a tarihin kwallon kafa.

    Da aka tambaye shi ko an cimma matsaya, Eberl ya ce: “An rubuta abubuwa da dama kuma rahotannin baya bayan nan game da Josko mu kan mu sun ba mu mamaki''.

    Ya kara da cewa "A halin da ake ciki yanzu akwai nisa tsakanin mu sosai.

    “Kamar yadda kuke gani, Josko yana nan – don haka ba gaskiya ba ne. "Bai yi gwajin lafiya ba - mu dai ba mu san da haka ba . “Babu wata yarjejeniya, ko kusa ba a yi ba'' in ji shi.

  10. Gasar cin kofin duniya: Switzerland ta yi nasara kan Philippines

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Switzerland ta bude gasar cin kofin duniya ta mata ta Fifa ta 2023 da ci 2-0 a kan Philippines a Dunedin, New Zealand.

    Fenaretin da Ramona Bachman ta ci daf da hutun rabin lokaci ne kwallon farko da Switzerland suka zura a ragar Philippines, kafin Seraina Piubel ta kara ta biyu a minti na 64 da fara wasa.

    Sakamakon ya sa Switzerland ta kasance kan gaba a rukunin A inda ta tsallake mai masaukin baki New Zealand.

    Yanzu Switzerland za ta kara da Norway a wasan ta na gaba a ranar 25 ga watan Yuli

  11. Gasar cin kofin duniya: Sifaniya ta lallasa Costa Rica

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Kasar Sifaniya ta samu nasara a gasar cin kofin duniya ta mata a inda ta lallasa Costa Rica 3-0 a wasansu da aka buga a Wellington.

    Sifaniya ta mamye wasan, inda ta yi yunkurin jefa kwallo 46, ita kuma Costa Rica wacce ke matsayi na 36 a duniya ta kai hari sau daya kacal.

    Sifaniya ta mallaki kashi 80% na kwallon ta kuma sami bugun kusurwa 22 idan aka kwatanta da guda daya kacal daga abokan karawarta.

    Sifaniya za ta sake neman wata babbar nasara a wasanta na gaba ranar 26 ga watan Yuli, yayin da za ta kara da Zambia, wacce ke matsayi mafi karanci a gasar, inda ita kuma Costa Rica za ta kara da Japan wadda ta lashe gasar a shekarar 2011.

  12. Burnley ta dauko Redmond

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Burnley ta tabbatar da daukar Nathan Redmond kan kwantiragin shekaru biyu bayan dan wasan ya bar Besiktas.

    Dan wasan mai shekaru 29, ya zura kwallaye shida a wasanni 28 a kakar wasan da ta wuce kuma yana da kwarewa a gasar Premier inda ya buga wasanni bakwai a Southampton.

    "Na dade ina da burin sake buga gasar Premier. Abin da Burnley ke yi yanzu ya dace da burina," in ji Redmond.

    Ya kara da cewa "Kulob din na da niyyar bunkasa wasana kuma sun fahimci darajar da zan iya kawowa a ciki da wajen fili''.

  13. An yi wa golan PSG Donnarumma fashi a Paris

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An kai wa golan Italiya da Paris St-Germain, Gianluigi Donnarumma da abokiyar zamansa hari tare da yi musu fashi a gidansu da ke birnin Paris.

    Wasu mutane da dama ne suka kai harin tare da daure su a gidansu da ke gunduma ta takwas a tsakiyar babban birnin kasar, kamar yadda majiyar 'yan sanda ta shaida wa kafar yada labaran Faransa.

    Daga nan aka ce sun tsere zuwa wani otal da ke kusa bayan maharan sun tafi.

    Ma’aikatan otal ne suka sanar wa 'yan sanda kafin aka kai su asibiti.

    Rahotannin da ba a tabbatar da su ba a shafin yada labarai na Actu17 sun ce maharan sun yi awon gaba da kayan ado da agoguna da kuma kayan alatu da kudinsu ya kai Yuro 500,000 .

    Dan wasan ya samu rauni kadan yayin da abokiyar zamansa, Alessia Elefante, ba ta ji rauni ba, kamar yadda majiyoyi suka shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Faransa.

  14. Danjuma zai koma Everton

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun bayyana cewa dan wasan kasar Netherlands Arnaut Danjuma na shirin komawa Everton aro daga Villarreal.

    An yi tsammanin dan wasan mai shekaru 26 zai koma Toffees a watan Janairu amma a maimakon haka ya koma Spurs a karshen tafiya.

    Danjuma ya buga wa Bournemouth daga shekarar 2019 zuwa 2021, inda ya zura kwallaye 17 a wasanni 52 kafin ya koma La Liga da Villareal.

    Ya buga wa kasarsa ta Netherlands wasanni shida, inda ya zura kwallaye biyu a raga, amma bai shiga cikin tawagar kasar Netherlands a gasar cin kofin duniya ta 2022 ba.