Jonathan ya nuna damuwa kan sabon tsarin zaɓe a Afirka ta Kudu
Tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan da ke jagorantar tawagar masu saka ido kan zaɓen Afrika ta Kudu ya bayyana damuwarsa kan sabon tsarin rajistar zaɓe na kasar.
Ya shaida wa BBC cewa "abin da muke fargaba a kai shi ne mutanen da ba su koma yankunansu don kada kuri'unsu ba".
"A da mutane na iya kaɗa ƙuri'unsu a manyan birane kamar Pretoria da Johannesburg da Cape Town ba tare da wata tangarda ba".
"Amma a wannan karon, duk wanda yake son kaɗa ƙuri'a a inda ba mazabarsa ba na bukatar ya nemi hukumar zabe da ta sake masa mazaba zuwa inda yake son kada kuri'ar".
Jonathan wanda ya jagoranci Najeriya daga 2010 zuwa 2015, ya ce da yawa daga cikin masu kada kuri'un ba su kammala wannan matakan ba, inda suke tunanin cewa za su iya yin zabe kamar yadda suka saba yi a baya.
Jagoran mai shekara 66 ya kara da cewa: "Rudani kan kirkirar sabon tsarin zaɓe da aka yi don ba wa 'yan takara masu zaman kansu dama a karon farko a tarihin Afrika ta kudu na iya janyo matsaloli."
Ya kuma ce ana bukatar wayar wa da mutane kai a mazaɓu wanda hakan zai kawo rashin sauri.