An kashe Falasɗinawa 46 cikin awa 24, a cewar ma'aikatar lafiyar Gaza
Ma'aikatar lafiya ƙarƙashin ikon Hamas ta ce an kashe Falasɗinawa aƙalla 46 cikin awa 24 da suka wuce a Zirin Gaza.
Hakan ya sa adadin mutanen da aka kashe a zirin tun daga ranar 7 ga watan Oktoba sun zama 36,096, in ji ta - sakamakon hare-haren Isra'ila.
Haka nan, an jikkata ƙarin mutum 110 tun daga Litinin ɗin.
Isra'ila ta ƙaddamar da hare-haren ne a masayin ramuwar gayya kan harin da mayaƙan Hamas suka kai mata, inda suka kashe mutum 1,200 da kuma sace sama da 250.
Yanzu haka Isra'ila ta mayar da hankali ne kan birnin Rafah da ke kudancin Gaza, inda take iƙirarin cewa nan ce tungar Hamas ta ƙarshe da take so ta tarwatsa.