Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/05/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 23 ga watan Mayun, 2024.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza, Umar Mikail and Haruna Kakangi

  1. Majalisar dokokin Kano ta fara zaman gyara dokar masarautu

    Majalisar dokokin Kano ta fara zaman gyara dokar da ta kafa sabbin masarautun jihar.

    Waɗansu majiyoyi masu ƙarfi sun tabbatar wa BBC cewa ‘yan majalisar za su soke dokar da aka yi a shekarar 2019, wadda ta bayar da damar kafa ƙarin manyan masarautu huɗu a cikin jihar.

  2. Mahamat Deby zai sha rantsuwar kama aiki

    Nan gaba a ayu ne za a gudanar da bikin rantsar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Chadi Mahamat Idriss Deby, bayan lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar 6 ga watan Mayu.

    Rantsuwar ce kuma za ta kawo ƙarshen mulkin riƙon ƙwarya da aka shafe shekara uku ana gudanarwa a ƙasar.

    Ana sa rana manyan baƙi ciki har da shugabannin ƙasashen duniya ne za su halarci bikin da za a gudanar a N'Djamena, babban birnin ƙasar.

    Hukumar zaɓen ƙasar ce ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashen zaɓen shugaban ƙasar bayan da ta ce ya samu kashi 61 na ƙuri'un da aka kaɗa.

    Sakamakon da jam'iyyun adawa cikin har da babban abokin hamayyarsa firaminista, Succes Masra suka yi watsi da shi, suna masu iƙirarin cewa akwai kura-kurai a ciki.

    A watan Aprilun 2021 ne Mahamat Idriss Deby ya ɗare karagar mulkin ƙasar bayan rasuwar mahaifinsa, Idris Deby Itno, da aka kashe a filin daga lokacin wani gumurzu da 'yan tawaye a arewacin ƙasar.

  3. CBN ya buƙaci masu canjin kuɗi su sabunta lasisinsu kafin Disamba

    Babban bankin Najeriya, CBN ya buƙaci masu musayar kuɗi a ƙasar su sake neman buƙatar sabunta lasisinsu.

    Cikin wata sanarwa da Babban Bankin ya fitar ranar Laraba, ya ce ya ɗauki matakin ne domin daidaita kasuwar musayar kuɗi don bunƙasa harkokinsu.

    CBN ɗin ya ce a yanzu mafi ƙarancin jarin da masu musayar kuɗi ya kamata su mallaka shi ne naira biliyan biyu ga 'yan rukunin farko na Tier 1, yayin da 'yan rukuni na biyu watau Tier 2 zai koma naira miliyan 500.

    Haka kuma sabuwar ƙa'idar da CBN ɗin ya fitar ta soke kuɗin ajiya na dole da masu rukunin farko suke ajiyewa na dole na naira miliyan 200, da kuma naira miliyan 50 na masu rukuni na biyu.

    Cikin Sanarwar ta CBN ɗin ya aike wa masu chanjin kuɗin, ta nuna cewa sabuwar dokar za ta fara aiki daga ranar 3 ga watan Yuni.

    CBN ɗin ya kuma bai wa masu musayar kuɗin wa'adin mako shida da su cika waɗannan sharuɗa.

  4. Tanadin dokar masarautun Kano ta 2019

    Dokar ta yi tanadi 51, kamar yadda majalisar dokokin jihar Kano ta bayyana a lokacin da ta yi wa dokar gyara a shekara ta 2019.

    Ga waɗansu muhimmai daga cikin su:

    • Gwamna ne zai zaɓi shugaban majalisar sarakuna da za a kafa nan gaba.
    • Gwamna ne zai naɗa masu zaɓar sarki a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
    • Duk sarkin da gwamna ya zaɓa don shugabantar majalisar sarakuna, zai jagorance ta ne tsawon shekara biyu.
    • Duk sarkin da ya ƙi halartar tarukan majalisar sarakunan har sau uku ba tare da ƙwaƙƙwaran dalili ba, ya kori kansa daga sarauta.
  5. China na gudanar da atisayen soji a kusa da Taiwan

    China na gudanar da atisayen soji na hain-gwiwa a kusa da Taiwan, kwanaki bayan rantsar da William Lai a matsayin sabon shugaban ƙasar ta Taiwan.

    Kakakin sojin China, ya ce gomman jiragen yaƙi ɗauke da makamai masu linzami sun rinƙa shawagi da gwada kai hari, da taimakon sojoji ruwa da masu kula da irin waɗanan makamai.

    Sojojin na China nuna cewa wannan atisaye ladabtarwa ne da gargaɗi mai ƙarfi ga 'yan aware a Taiwan tare da gargaɗin kada kowa ya tsoma bakinsa ko ya yi musu katsalanda daga ketare.

    Taiwan dai ta tattaro kan sojojinta tana kuma mai tabbatar da cewa za ta iya kare tsibirinta.

  6. Ana sa ran majalisar dokokin Kano za ta kammala aiki a kan dokar masarautu a yau

    Bayanan da ke fitowa daga majalisar dokokin jihar Kano a arewacin Najeriya na cewa a yau ne ‘yan majalisar za su kammala aiki a kan dokar da ta kafa sabbin masarautu a jihar.

    Waɗansu majiyoyi masu ƙarfi sun tabbatar wa BBC cewa ‘yan majalisar za su soke dokar da aka yi a shekarar 2019, wadda ta bayar da damar kafa ƙarin manyan masarautu huɗu a cikin jihar.

    Dokar ta ƙirkiri masarautar Bichi da ta Karaye da ta Gaya da kuma masarautar Rano.Tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ne ya sanya hannu a dokar a watan Disambar 2019.

    A halin yanzu dai an girke jami‘an tsaro a wurare da dama na birnin Kano domin kauce wa tashin hankali.

    Waɗansu majiyoyi a Kano ɗin sun tabbatar da cewa da zarar majalisar ta kammala kwaskwarima a kan dokar, ba tare da ɓata lokaci ba za ta mika wa gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf.

    Kuma ana sa ran gwamnan na Kano zai sanya hannu a kan dokar kafin sanar da rushe sabbin masarautun da aka kafa a shekara ta 2019.

  7. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye, barkamu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a dai dai wannan lokaci domin kawo muku irin wainar da ake toyawa a faɗin duniya, musamman Najeriya da makwabtan ƙasashe.

    Kuna kuma iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawar a shafukanmu na sada zumunta.