Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/05/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 23 ga watan Mayun, 2024.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza, Umar Mikail and Haruna Kakangi

  1. An yaɗa dubban sauro masu yaƙi da Maleriya a Djibouti

    Dubun dubatar sauro, waɗanda aka jirkita wa ƙwayoyin halitta ne aka saki a ƙasar Djibouti, a wani yunƙuri na yaƙi da yaɗuwar nau'in sauro mai yaɗa cutar maleriya.

    Sabbin sauron jinsin maza da aka saki waɗanda wani kamfanin kula da halittu na Birtaniya ya samar - na ɗauke da wani sanadari da ke kashe sauro jinsin mata kafin su girma.

    Nau'in sauron da aka saki ba ya cizo kuma ba ya cutar da al'imma.

    Sauro jinsin mata ne kawai ke cizo tare da sanya wa mutane cutar zazzaɓi.

    Wannan karo na farko da aka saki irin waɗannan sauro a yankin gabashin nahiyar Afirka, kuma karo na biyu a faɗin nahiyar Afirka.

    Amurka ta ce an yi amfani da irin wannan tsari a Brazil da tsibirin Cayman da Panama da kuma Indiya, kuma ya yi aiki yadda ya kamata.

  2. An rantsar da Mahamat Deby a matsayin sabon shugaban Chadi

    An rantsar da Janar Mahamat Deby a matsayin sabon shugaban ƙasar Chadi, bayan wani zaɓe mai cike da zargin maguɗi, wanda ya kawo ƙarshen mulkin riƙon ƙwaryar ƙasar na shekara uku.

    Lokacin rantsar da shi, Deby ya yi alƙawarin "karewa tare da yin biyayya ga dokoki da kundin tsarin mulkin ƙasar, tare kuma da sauke nauyin da ƙasar ta ɗora masa".

    Haka nan Janar Deby ya kuma sha alwashin "tabbatar da an yi wa dukkanin al;ummar Chadi adalci, tare da kare haƙƙoƙi da ƴancin kowane ɗan ƙasa."

    Rantsuwar da ya sha ta yau na nufin ya fara wa'adin mulkin ƙasar na shekara biyar tare da dawowar mulkin demokuraɗiyya a ƙasar.

    Shugabannin ƙasashen Afirka da suka halarci bikin rantsuwar sun haɗa da Bola Tinubu na Najeriya, Brice Olihui Nguema na Gabon, Umaro Sissoco Embalo na Guinea Bissau da kuma Faustin-Archange Touadera na Jamhuriyar Demokuɗiyyar Congo.

    An bayyana Mahamat Deby a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa ne da ƙuri'u mafi yawa da suka kai kashi 61%, duk da cewa ɗan takarar adawa kuma firaminista Succes Masra ya ƙalubalanci sakamakon.

  3. An bai wa tsofaffin sarakunan Kano sa'o'i 48 su fice daga masarautu

    Gwamnatin jihar Kano ta bai wa tsofaffin sarakunan masarautun Kano, Rano, Gaya, Bichi da Karaye wa'adin sa'o'i 48 su fice daga fada bayan rushe masarautun da gwamnatin ta yi a yau Alhamis.

    Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ne ya sanar da haka lokacin da ya yi jawabi jim kaɗan bayan sanya hannu kan dokar da ta rushe dokar da ta assasa masarautun a shekara ta 2019.

    A yau Alhamis ne gwamnan ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautar Kano, wadda ta rushe ƙarin masarautu huɗu da aka samar a 2019, wanda hakan ya sanya suka rasa muƙamansu na sarakunan jihar masu daraja ta ɗaya.

    Gwamna Abba Kabir ya ce "Ina umartar sarakunan da dokar ta shafa su fice daga fadojin cikin sa'o'i 48".

    Sarakunan da aka sauke su ne:

    Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

    Sarkin Bichi Nasiru Ado Bayero

    Sarkin Rano Kabiru Muhammad Inuwa

    Sarkin Gaya Aliyu Ibrahim Abdulkadir

    Sarkin Karaye Dr Ibrahim Abubakar

  4. Yadda Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya sake komawa kan karaga

  5. An mayar da Muhammadu Sanusi II kan muƙamin sarkin Kano

    Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sanar da mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin sarkin Kano.

    Gwamnan ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan sanya hannu kan dokar da ta yi gyara ga dokar da ta kafa masarautun Kano guda biyar ta 2019.

    A yau Alhamis ne Majalisar dokokin ta jihar Kano ta yi wa ƙudurin dokar soke masarautu biyar na Kano - wato Kano, Bichi, Rano, Karaye da Gaya karatu na uku tare da amincewa da ita.

    Daga nan ne aka miƙa dokar ga gwamnan wanda ya sanya mata hannu.

    A lokacin jawabin da ya yi, Gwamna Kabir ya ce: "Bayan soke dokar masarautu ta jihar Kano ta 2019, hakan na nufin cewa masarautar Kano ta koma matsayinta gabanin dokar ta 2019".

    Ya ƙara da cewa "hakan na nufin babu wani halastaccen sarki a Kano face Sarki Muhammadu Sanusi".

    A shekara ta 2019 ne gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ta samar da dokar kafa masarautu biyar.

    Haka nan a ranar 9 ga watan Maris ɗin 2020 ne aka sauke sarkin Kano na 14 Muhammadu Sanusi II daga karaga bayan rashin jituwa tsakaninsa da gwamnatin jihar.

    • Tarihin Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II
  6. Abba Kabir ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautun Kano

    Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautu da majalisar dokokin jihar ta yi wa kwaskwarima.

    Tawagar 'yan majalisar ƙarƙashin jagorancin kakakain majalisar Jibril Isma'il Falgore ne suka gabatar wa gwamnan sabuwar dokar a gidan gwamnatin jihar.

    Da safiyar yau Alhamis ne dai majalisar ta yi wa dokar masarautun Kano ta shekarar 2019 kwaskwarima, inda ta soke duka masarautun jihar biyar.

    Wakilin BBC da ke gidan gamnatin jihar ya ce tuni masu zaɓen sarki suka isa gidan gwamnatin jihar, a shirye-shiryen da ake yi na zaɓen sabon sarki.

  7. An binne tsohon shugaban Iran Ebrahim Raisi

    An binne tsohon shugaban Iran Ebrahim Raisi a birnin Mashhad, na biyu mafi girma a ƙasar kuma mahaifarsa.

    Raisi ya rasu ne ranar Lahadi sanadiyyar hatsarin jirgin sama, tare da ministan harkokin waje na ƙasar da kuma wasu mutanen shidda.

    Dubban mutane ne suka kwarara a kan titunan birnin na Mashhad domin nuna alhini da rasuwar tasa.

    Sun riƙa jefa furanni kan motar da ke ɗauke da gawarsa yayin da rake kan hanyar maƙabartar Imam Reza, wuri mai matuƙar tsarki a Iran.

    Yanzu hankali zai koma kan wanda zai gaji Raisi, wanda kafin rasuwarsa aka yi zaton cewa shi ne zai gaji jagoran musulunci na ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei.

  8. Hotunan masu zaɓen sarki a lokacin da suka isa gidan gwamnatin Kano

  9. Majalisar dokokin Kano ta miƙa wa gwamna sabuwar dokar masarautu

    Kakakin majalisar dokokin jihar Kano, Jibril Falgore tare da rakiyar wasu jagororin majalisar sun isa gidan gwamnati domin kai wa gwamna sabuwar dokar masarautu da majalisar ta yi wa kwaskwarima.

    Dazu da safe ne majalisar ta yi wa dokar masarautun jihar ta shekara 2019 kwaskwarima, inda ta soke duka masarautun jihar biyar.

    Wakilin BBC da ke Kano ya ce a halin da ake ciki gwamnan tare da 'yan majalisar suna cin abincin rana ne a gidan gwamnati, inda ake sa ran gwamnan zai saka hannu kan sabuwar dokar da zarar sun kammala cin abincin.

    Wasu majiyoyi a gidan gwamnatin sun shaida wa wakilin namu cewa tuni masu zaɓen sarki a Kano suka isa fadar gwamnatin jihar, wataƙila domin shirye-shiryen zaɓen sabon sarki.

  10. Ya kamata a riƙa sassauta wa mutane haraji - Muhammadu Sanusi ll

    Sarkin Kano na 14 Muhammadu Sanusi ll, ya ce ya kamata gwamnati ta riƙa cizawa tana hurawa game da haraje-harajen da take ƙaƙaba wa al'umma.

    Muhammadu Sanusi ll ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron kan tattalin arziki da zuba jari na 2024 da aka gudanar a birnin Fatakwal na jihar Rivers.

    Ya kafa hujja da maganar tsohuwar firaministan Birtaniya, Margaret Thatcher, wadda take cewa babu ƙasar da da za ta samar da ci gaba ta hanyar tatsar al'ummarta.

    Ya ce duk da cewa karɓar haraji na da muhimmanci, amma bai kamata a tsawwala wa jama'a ba, ''ya kamata gwamnati ta karɓi haraji domin ci gaban ƙasa, ba domin samun riba ba''.

  11. Abubuwan da sabuwar dokar masarautun Kano ta 2024 ta ƙunsa

  12. Shugabannin ƙasashe na halartar bikin rantsar da Mahamat Deby a Chadi

    Shugabannin ƙasashen duniya da dama ne suka hallara a N,jamena, babban birnin Chadi domin halartar bikin rantsar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Mahamat Idris Deby, bayan nasarar da ya samu a zaɓen shugabann ƙasar da ya gudana cikin wannan wata.

    Rantsar da shugaban ƙasar zai kawo ƙarshen mulkin riƙon ƙwarya da aka shafe shekara uku ana gudanarwa a ƙasar.

    Mista Deby ya samu nasara da kashi 61, a zaɓen da mafi yawan 'yan adawa suka yi watsi da shi.

    Ƙungiyoyin duniya da dama da suka sanya idanu a zaɓen sun ce zaɓen ƙasar ya gudana ne ba yabo ba fallasa.

  13. Gawar Raisi ta isa garin da za a binne shi

    Gawar marigayi tsohon shugaban Iran Ebrahim Raisi ta isa mahaifarsa birnin Mashhad inda a nan ne za a binne shi.

    Tsohon shugaban ƙasar ya rasu ne a hatsarin jirgi mai saukar ungulu ranar Lahadi tare da ministan harkokin wajen ƙasar Hossein Amir-Abdollahian, da wasu mutum shida.

    Jami'ai a birnin Mashhad sun taru domin raka gawar marigayin zuwa maƙabarta, inda jama'a da dama ke riƙe da fitattun hotunansa da kuma baƙaƙen tutoci masu ɗauke da rubutun kalmomin Larabci.

    Tun da farko dubban Iraniyawa ne suka taru a birnin Birjand domin yin bankwana da gawar tsohon shugaban ƙasar.

  14. Mutum shida sun mutu bayan harin da Rasha ta kai Kharkiv

    Aƙalla mutum shida ne suka mutu yayin da gommai suka jikkata bayan da Rasha ta kai harin makamai mai linzami zuwa garin Kharkiv da ke arewa maso gabashin Ukraine.

    Gwamnan yankin,Oleg Sinegubov ya ce har yanzu ba a san inda mutum biyu suka shiga ba, bayan harin da dakarun Rasha suka kai wa birni na biyu mafi girma a Ukraine aƙalla sau 15.

    Gwamnan ya yi kira ga mazauna birnin da su zauna a gidanjensu.

    Hukumar sufurijn jiragen ƙasa ta Ukraine ta ce harin ya lalata mafi yawan ɓangarorin layin dogo da ke birnin, yayin da ma'aikatanta da dama suka jikkata.

    A farkon wannan wata ne dakarun Rasha suka sabunta kai hare-hare a yankin a yunƙurin da suke yi durƙusar da dakaraun Ukraine.

    A ranar Laraba ne mista Sinegubov ya ce an ci gaba da gwambza faɗa a garuruwan Pletenivka da Vovchansk, to sai dai ya ce dakarun ƙasar ne ke iko da garuruwan.

  15. Mutum 11 sun mutu bayan wata fashewa a masana'antar siga a Tanzaniya

    Hukumomi a Tanzaniya sun ce mutum 11 ne suka mutu, yayin da wasu biyu suka jikkata bayan wata fashewa da ta auku a masana'antar sarrafa siga ta Mvomero da ke yammacin Tanzania a cewar mahukunta.

    Lamarin ya faru ne a yankin Morogoro mai tazarar kilomita 370 daga Dar es Salaam, babban birnin ƙasar wanda ya kasance gari mafi girma a fannin kasuwanci a ƙasar.

    Kwamishina a hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar, Alex Mkama ya ce "a cikin daren jiya an samu fashewar wani abu da misalain ƙarfe 11:00 na dare''.

    Hukumomin ƙasar sunj ce daga cikin waɗanda suka rasun akwai ƴan asalin ƙasar Brazil da Indiya da China da kuma Kenya.

  16. Mafi ƙarancin albashi: NLC ta nemi gwamnati ta biya N497,000 maimakon 615,000

    Ƙungiyoyin ƴan ƙwadago na NLC da TUC sun sassauta abin da suke buƙata gwamnati ta biya a matsayin mafi ƙarancin albashi a ƙasar zuwa naira 497,000.

    A baya dai ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce amince da naira 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi da suke son gwamnatin ƙasar ta amiince da shi.

    Yayin cigaba da tattaunawar a ranar Talata, ƙungiyoyin sun kuma yi watsi da sabon ƙudirin da gwamnati ta gabatar na naira 54,000 a matsayin albashi mafi ƙaranci.

    Haka kuma a ranar Laraba kwamitin ƙarin albashin ya bai wa NLC tayin naira 57,000 a matsayin mafi ƙarancin albashin, inda nan take ƙungiyar ƙwadagon ta yi fatali da tayin.

  17. An kuɓutar da 'ya'yan ɗan majalisar Zamfara bayan wata 17 da sace su

    Ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro tare da hadin gwiwar ƴan sanda sun ceto 'ya'ya mata biyu na wani ɗan majalisar jihar Zamfara da aka yi garkuwa da su wata 17 da suka gabata.

    Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa a ranar Talata ne aka miƙa yaran biyu, Maryam da Nana Asma'u ga mahaifin nasu Aminu Ardo a hedikwatar ƴan sanda ta ƙasa da ke birnin Abuja.

    A lokacin miƙa wa ɗan majalisar 'ya'yan nasa, mataimakin jami'in hulɗa da jama'a na rundunar, CSP Isuku Victor ya ce mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro Mallam Nuhu Ribaɗo ne ya jagoranci ƙoƙarin ceto yaran tare da haɗin gwiwar jami'an tsaro.

    A watan Nuwanbar 2022 ne ƴan bindiga suka kai hari gidan Aminu Ardo a Jangebe da ke jihar Zamfara tare da yin garkuwa da matarsa da kuma ƙananan yaransa huɗu.

    Mahaifiyar yaran da kuma biyu daga cikin yaran sun samu kuɓuta bayan da rahotonni sujka ce sun gudu daga inda ['yan bindigar suka tsare su, inda suka bar sauran biyun Maryam da Nana Asma'u a hannun masu garkuwar.

    CSP Victor ya ce yaran sun fuskanci wahalar rayuwa a lokacin da suke tsare a hannun 'yan bindigar ciki har da shan ruwan rafuka.

  18. Majalisar Kano ta rushe masarautu biyar na jihar

  19. Ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar za su janye ficewa daga Ecowas

    Ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar na shirin janye matakinsu na ficewa daga ƙungiyar Ecowas mai raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma.

    Sanata Ali Ndume - wanda ɗan majalisar ƙungiyar Ecowas ɗin ne - ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a Kano, a yayin da majalisar ƙungiyar ke ci gaba da gudanar da taronta a jihar.

    Dan majalisar ya ce an cimma duk wani abu da ake buƙata domin maido da ƙasashen cikin ƙungiyar ta Ecowas.

    "An riga an warware saɓanin da ya kai ga ɗaukar matakin fita daga ƙungiyar, kuma a yanzu duka ƙasashen sun huce daga fushin da suke yi da Ecowas, saboda haka ga dukkan alamu a shirye suka su dawo cikin ƙungiyar'', in ji ɗan majalisar.

    Ƙasashen uku sun ɗauki matakin fita daga ƙungiyar ne bayan da Ecowas ta yi Allah wadai da juyin mulkin da sojoji sukayi a ƙasashen, tare da sanya musu jerin takunkumai.

  20. NLC ta sake fatali da tayin N57,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

    Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya NLC ta sake yin watsi da tayin naira 57,000 a matsayin mafi ƙarncin albashi a ƙasar da kwamitin ƙarin albashin ya yi mata.

    Wannan ne karo na uku da NLC ke watsi da ƙarin da gwamnatin ta yi masa cikin kusan mako guda.

    A ranar Talata ne NLC ta yi watsi da tayin naira 54,000 da gwamnatin ƙasar ta yi wa ma'aikatan ƙasar, bayan da a makon da ya gabata ƙungiyar ta ƙi amincewa da tayin naira 48,000 daga ɓangaren gwamnatin ƙasar.

    Ƙungiyar dai ta bai wa gwamnatin ƙasar wa'adin zuwa ranar 31 ga watan Mayun da muke ciki domin cimma matsaya kan mafi ƙarancin albashin.