An sanya lokacin gudanar da sabon zaɓe a Iran bayan mutuwar Shugaba Raisi
Kafafen yada labarai a Iran sun ce za a gudanar da zaben shugaban kasa nan da ranar 28 ga watan Yunin gobe, bayan mutuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi.
Raisi ya rasu ne a ranar Lahadi sakamakon hadarin jirgin da ya rutsa da shi tare da Ministan harkokin wajen kasar Hossein Amirabdollahian.
Shugaban sojin kasar ya bayar da umarnin a gudanar da binciken dalilin hatsarin jirgin.
Gabanin zaben an ayyana mataimakin Raisi, Muhammad Mukhbir a matsayin wanda zai ci gaba da jagorantar kasar.
An kuma nada tsohon kwararen mai shiga tsakanin kan makamin nukiliya Ali Bageri a matsayin sabon ministan harkokin wajen Iran.